< Ayuba 33 >
1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
Nun aber höre, Hiob, meine Rede und allen meinen Worten leih' dein Ohr.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Siehe doch, ich thue meinen Mund auf, und meine Zunge redet unter meinem Gaumen.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
Geradem Sinn entstammen meine Worte, und was meine Lippen wissen, sprechen sie lauter aus.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
Der Geist Gottes hat mich geschaffen, und des Allmächtigen Odem belebt mich.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Wenn du kannst, so widerlege mich; rüste dich gegen mich, stelle dich zum Kampf.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Siehe, ich stehe zu Gott, wie du; aus gleichem Thon wie du bin ich geschnitten.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Nein, Furcht vor mir braucht dich nicht zu erschrecken, und meine Hand soll dich nicht niederdrücken.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Allein, vor meinen Ohren sagtest du - ich vernahm den Laut deiner Worte:
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
“Rein bin ich, ohne Missethat, bin lauter und frei von Schuld.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Fürwahr, Feindseligkeiten erfindet er gegen mich, erachtet mich für seinen Feind,
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
legt meine Füße in den Block, beobachtet alle meine Wege.”
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Sieh, darin hast du Unrecht, erwidere ich dir; denn Gott ist größer als ein Mensch.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Warum hast du gegen ihn gehadert, daß er auf alle deine Worte keine Antwort erteile?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
Denn freilich spricht Gott einmal, auch zweimal - aber man beachtet es nicht.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
Im Traum, im Nachtgesicht, wenn tiefer Schlaf auf die Menschen fällt, im Schlummer auf dem Lager,
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
dann öffnet er der Menschen Ohr und drückt ihrer Verwarnung das Siegel auf,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
von seinem Thun den Menschen abzubringen und den Mann vor Hoffart zu schirmen.
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
Er bewahrt seine Seele vor der Grube und sein Leben, daß es nicht durch Geschosse dahinfährt.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
Auch wird er gezüchtigt durch Schmerz auf seinem Lager; ununterbrochen wütet der Kampf in seinem Gebein.
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
Dann läßt ihm sein Lebenstrieb das Brot zum Ekel werden, und seine Seele die Lieblingsspeise.
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
Sein Fleisch schwindet dahin, daß es kein Ansehen mehr hat, unscheinbar wird sein dürres Gebein,
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
so daß seine Seele dem Grabe nahe ist, und sein Leben den Todesengeln.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
Wenn dann ein Fürsprech-Engel für ihn da ist, einer von den Tausend, dem Menschen seine Pflicht zu verkündigen,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
und er sich seiner erbarmt und spricht: “Erlöse ihn und laß ihn nicht in die Grube hinabfahren; ich habe das Lösegeld erhalten” -
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
dann strotzt sein Leib von Jugendfrische, er kehrt zurück zu den Tagen seiner Jugendkraft.
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
Er fleht zu Gott, und der erweist ihm Gnade, läßt ihm sein Antlitz unter Jauchzen schauen und vergilt so dem Menschen sein richtiges Verhalten.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Er singt vor den Leuten und spricht: “Ich hatte gesündigt und das Recht verkehrt, doch wurde es mir nicht vergolten.
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
Er hat meine Seele erlöst und sie nicht zur Grube hinfahren lassen, und mein Leben erfreut sich am Licht.”
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Sieh, dies alles thut Gott mit dem Menschen zweimal, dreimal,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
seine Seele der Grube zu entreißen, daß er vom Lichte des Lebens umleuchtet werde.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Merke auf, Hiob, höre mir zu; schweige und laß mich reden!
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Hast du Worte, so widerlege mich; sprich nur, denn gern gäbe ich dir Recht!
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
Wo nicht, so höre du mir zu; schweige, damit ich dich Weisheit lehre.