< Ayuba 33 >

1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
Or, donc, écoute, Job, mon discours, prête ton attention à toutes mes paroles.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Vois, je vais ouvrir la bouche et laisser parler ma langue dans mon palais.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
La droiture de mon cœur respire dans mes paroles, et mes lèvres diront clairement ce que je sais.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
L’Esprit de Dieu m’a créé, le souffle de Dieu soutient ma vie.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Si tu le peux, tu me réfuteras; oppose-moi tes raisons, tiens-moi tête.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Vois, je suis comme toi au regard de Dieu: je suis pétri d’argile, moi aussi.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Tu n’as donc pas à trembler devant moi, et mon autorité ne pèsera pas lourdement sur toi.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Mais tu as dit à mes oreilles j’entends encore le son de tes paroles:
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
"Je suis pur, sans péché; je suis à l’abri de tout blâme, n’ayant point commis de faute.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Mais quoi! Dieu trouve des griefs contre moi, il me considère comme son ennemi.
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
Il emprisonne mes pieds dans les ceps, surveille toutes mes voies!"
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
"Certes, en cela tu n’as pas raison, te répliquerai-je, car Dieu est plus grand que l’homme."
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Pourquoi entres-tu en lutte avec lui, sous prétexte qu’il ne rend compte d’aucun de ses décrets?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
A la vérité, Dieu parle une fois, même deux fois; on n’y fait pas attention!
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
En songe, dans des visions nocturnes, lorsqu’un profond sommeil s’empare des hommes, lorsqu’ils dorment sur leurs couches,
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
alors il ouvre l’oreille des mortels, et met son sceau sur la correction qu’il leur inflige,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
pour détourner les gens de leurs agissements et protéger les puissants contre l’orgueil.
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
Ainsi il préserve leur âme de la perdition et empêche leur vie de succomber sous le glaive.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
L’Homme est éprouvé par la souffrance sur sa couche, alors que la plupart de ses os demeurent intacts.
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
Tout son être a le dégoût de la nourriture, son âme repousse les mets les plus délicieux.
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
Sa chair se consume et disparaît à la vue; ses os, qui étaient invisibles, deviennent saillants.
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
Son âme est tout près de la tombe; sa vie semble livrée aux agents de la mort.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
S’Il est alors un ange qui intercède pour lui, un seul entre mille, qui révèle à l’homme son devoir,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
qui le prenne en pitié et dise: "Fais-lui grâce, pour qu’il ne descende pas dans la fosse, j’ai obtenu sa rançon",
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
alors sa chair retrouve la sève de la jeunesse, il est rendu aux jours de son adolescence.
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
Il implore Dieu, qui l’écoute avec bienveillance et lui permet de voir sa face avec des cris d’allégresse; il rémunère ainsi la droiture du mortel.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Celui-ci promène ses regards sur les hommes et dit: "J’Avais péché, violé le droit, et cela n’était pas bien de ma part.
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
Mais Dieu a exempté mon âme de descendre dans la fosse, ma vie jouira encore de la lumière."
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Voyez, tout cela, Dieu le fait deux ou trois fois en faveur de l’homme,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
pour ramener son âme des bords de l’abîme, et l’éclairer de la lumière des vivants.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Sois attentif, Job, écoute-moi; fais silence et laisse-moi parler.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Si tu as quelque chose à dire, réplique-moi; parle, car je souhaite te voir justifié.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
Si non, c’est à toi à m’écouter; tais-toi, et je t’enseignerai la sagesse.

< Ayuba 33 >