< Ayuba 33 >
1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
Maintenant donc, Job, écoute mes paroles, prête l’oreille à tous mes discours.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Voilà que j’ouvre la bouche, ma langue forme des mots dans mon palais,
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
mes paroles partiront d’un cœur droit, c’est la vérité pure qu’exprimeront mes lèvres.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
L’esprit de Dieu m’a créé, le souffle du Tout-Puissant me donne la vie.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Si tu le peux, réponds-moi; dispose tes arguments devant moi, tiens-toi ferme.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Devant Dieu je suis ton égal, comme toi j’ai été formé du limon.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Ainsi ma crainte ne t’épouvantera pas, et le poids de ma majesté ne peut t’accabler.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Oui, tu as dit à mes oreilles, et j’ai bien entendu le son de tes paroles;
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
« Je suis pur, exempt de tout péché; je suis irréprochable, il n’y a pas d’iniquité en moi.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Et Dieu invente contre moi des motifs de haine, il me traite comme son ennemi.
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
Il a mis mes pieds dans les ceps, il surveille tous mes pas. »
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Je te répondrai qu’en cela tu n’as pas été juste, car Dieu est plus grand que l’homme.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Pourquoi disputer contre lui, parce qu’il ne rend compte de ses actes à personne?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
Pourtant Dieu parle tantôt d’une manière, tantôt d’une autre, et l’on n’y fait pas attention.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
Il parle par des songes, par des visions nocturnes, quand un profond sommeil pèse sur les mortels, quand ils dorment sur leur couche.
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
A ce moment, il ouvre l’oreille des hommes, et y scelle ses avertissements,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
afin de détourner l’homme de ses œuvres mauvaises, et d’écarter de lui l’orgueil,
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
afin de sauver son âme de la mort, sa vie des atteintes du dard.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
Par la douleur aussi l’homme est repris sur sa couche, quand une lutte continue agite ses os.
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
Alors il prend en dégoût le pain, et il a horreur des mets exquis,
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
Sa chair s’évanouit aux regards, ses os qu’on ne voyait pas sont mis à nu.
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
Il s’approche de la fosse, sa vie est en proie aux horreurs du trépas.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
Mais s’il trouve pour intercesseur, un ange entre mille, qui fasse connaître à l’homme son devoir,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
Dieu a pitié de lui et dit à l’ange: « Epargne-lui de descendre dans la fosse, j’ai trouvé la rançon de sa vie. »
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
Sa chair alors a plus de fraîcheur qu’au premier âge, il revient aux jours de sa jeunesse.
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
Il prie Dieu, et Dieu lui est propice; il contemple sa face avec allégresse, et le Très-Haut lui rend son innocence.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Il chante parmi les hommes, il dit: « J’ai péché, j’ai violé la justice, et Dieu ne m’a pas traité selon mes fautes.
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
Il a épargné à mon âme de descendre dans la fosse, et ma vie s’épanouit à la lumière! »
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Voilà, Dieu fait tout cela, deux fois, trois fois, pour l’homme,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
afin de le ramener de la mort, de l’éclairer de la lumière des vivants.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Sois attentif, Job, écoute-moi; garde le silence, que je parle.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Si tu as quelque chose à dire, réponds-moi; parle, car je voudrais te trouver juste.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
Si tu n’as rien à dire, écoute-moi; fais silence, et je t’enseignerai la sagesse.