< Ayuba 33 >

1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
Howbeit, Job, I pray thee, hear my speech, and hearken to all my words.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Behold now, I have opened my mouth, my tongue hath spoken in my mouth.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
My words [shall utter] the uprightness of my heart: and that which my lips know they shall speak sincerely.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
The spirit of God hath made me, and the breath of the Almighty giveth me life.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
If thou canst, answer thou me; set [thy words] in order before me, stand forth.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Behold, I am toward God even as thou art: I also am formed out of the clay.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Behold, my terror shall not make thee afraid, neither shall my pressure be heavy upon thee.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Surely thou hast spoken in mine hearing, and I have heard the voice of [thy] words, [saying],
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
I am clean, without transgression; I am innocent, neither is there iniquity in me:
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Behold, he findeth occasions against me, he counteth me for his enemy;
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
He putteth my feet in the stocks, he marketh all my paths.
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Behold, I will answer thee, in this thou art not just; for God is greater than man.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Why dost thou strive against him? for he giveth not account of any of his matters.
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
For God speaketh once, yea twice, [though man] regardeth it not.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
In a dream, in a vision of the night, when deep sleep falleth upon men, in slumberings upon the bed;
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
Then he openeth the ears of men, and sealeth their instruction,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
That he may withdraw man [from his] purpose, and hide pride from man;
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
He keepeth back his soul from the pit, and his life from perishing by the sword.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
He is chastened also with pain upon his bed, and with continual strife in his bones:
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
So that his life abhorreth bread, and his soul dainty meat.
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
His flesh is consumed away, that it cannot be seen; and his bones that were not seen stick out.
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
Yea, his soul draweth near unto the pit, and his life to the destroyers.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
If there be with him an angel, an interpreter, one among a thousand, to shew unto man what is right for him;
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
Then he is gracious unto him, and saith, Deliver him from going down to the pit, I have found a ransom.
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
His flesh shall be fresher than a child’s; he returneth to the days of his youth:
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
He prayeth unto God, and he is favourable unto him; so that he seeth his face with joy: and he restoreth unto man his righteousness.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
He singeth before men, and saith, I have sinned, and perverted that which was right, and it profited me not:
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
He hath redeemed my soul from going into the pit, and my life shall behold the light.
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Lo, all these things doth God work, twice, [yea] thrice, with a man,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
To bring back his soul from the pit, that he may be enlightened with the light of the living.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Mark well, O Job, hearken unto me: hold thy peace, and I will speak.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
If thou hast any thing to say, answer me: speak, for I desire to justify thee.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
If not, hearken thou unto me: hold thy peace, and I will teach thee wisdom.

< Ayuba 33 >