< Ayuba 33 >
1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
“And yet, please, O Job, Hear my speech and give ear [to] all my words.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Now behold, I have opened my mouth, My tongue has spoken in the palate.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
Of the uprightness of my heart [are] my sayings, And my lips have clearly spoken knowledge.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
The Spirit of God has made me, And the breath of the Mighty quickens me.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
If you are able—answer me, Set in array before me—station yourself.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Behold, I [am], according to your word, for God, I have also been formed from the clay.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Behold, my terror does not frighten you, And my burden on you is not heavy.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Surely you have spoken in my ears, And the sounds of words I hear:
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
I [am] pure, without transgression, I [am] innocent, and I have no iniquity.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Behold, He develops hindrances against me, He reckons me for an enemy to Him,
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
He puts my feet in the stocks, He watches all my paths.
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Behold, you have not been righteous [in] this, I answer you, that God is greater than man.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Why have you striven against Him, When [for] all His matters He does not answer?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
For once God speaks, and twice (he does not behold it),
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
In a dream—a vision of night, In the falling of deep sleep on men, In slumberings on a bed.
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
Then He uncovers the ear of men, And seals for their instruction,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
To turn aside man [from] doing, And He conceals pride from man.
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
He keeps back his soul from corruption, And his life from passing away by a dart.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
And he has been reproved With pain on his bed, And the strife of his bones [is] enduring.
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
And his life has nauseated bread, And his soul desirable food.
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
His flesh is consumed from being seen, And his bones are high, they were not seen!
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
And his soul draws near to the pit, And his life to those causing death.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
If there is a messenger by him, An interpreter—one of a thousand, To declare for man his uprightness,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
Then He favors him and says, Ransom him from going down to the pit, I have found an atonement.
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
Fresher [is] his flesh than a child’s, He returns to the days of his youth.
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
He makes supplication to God, And He accepts him. And he sees His face with shouting, And He returns to man His righteousness.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
[Then] he looks on men and says, I sinned, and I have perverted uprightness, And it has not been profitable to me.
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
He has ransomed my soul From going over into the pit, And my life looks on the light.
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Behold, God works all these, Twice, [even] three times with man,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
To bring back his soul from the pit, To be enlightened with the light of the living.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Attend, O Job, listen to me, Keep silent, and I speak.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
If there are words—answer me, Speak, for I have a desire to justify you.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
If there are not—listen to me, Keep silent, and I teach you wisdom.”