< Ayuba 33 >

1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
“But now, O Job, hear my speech, and listen to all my words.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Behold, I will open my mouth; my address is on the tip of my tongue.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
My words are from an upright heart, and my lips speak sincerely what I know.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
The Spirit of God has made me, and the breath of the Almighty gives me life.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Refute me if you can; prepare your case and confront me.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
I am just like you before God; I was also formed from clay.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Surely no fear of me should terrify you; nor will my hand be heavy upon you.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Surely you have spoken in my hearing, and I have heard these very words:
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
‘I am pure, without transgression; I am clean, with no iniquity in me.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Yet God finds occasions against me; He counts me as His enemy.
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
He puts my feet in the stocks; He watches over all my paths.’
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Behold, you are not right in this matter. I will answer you, for God is greater than man.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Why do you complain to Him that He answers nothing a man asks?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
For God speaks in one way and in another, yet no one notices.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
In a dream, in a vision in the night, when deep sleep falls upon men as they slumber on their beds,
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
He opens their ears and terrifies them with warnings
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
to turn a man from wrongdoing and keep him from pride,
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
to preserve his soul from the Pit and his life from perishing by the sword.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
A man is also chastened on his bed with pain and constant distress in his bones,
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
so that he detests his bread, and his soul loathes his favorite food.
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
His flesh wastes away from sight, and his hidden bones protrude.
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
He draws near to the Pit, and his life to the messengers of death.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
Yet if there is a messenger on his side, one mediator in a thousand, to tell a man what is right for him,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
to be gracious to him and say, ‘Spare him from going down to the Pit; I have found his ransom,’
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
then his flesh is refreshed like a child’s; he returns to the days of his youth.
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
He prays to God and finds favor; he sees God’s face and shouts for joy, and God restores His righteousness to that man.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Then he sings before men with these words: ‘I have sinned and perverted what was right; yet I did not get what I deserved.
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
He redeemed my soul from going down to the Pit, and I will live to see the light.’
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Behold, all these things God does to a man, two or even three times,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
to bring back his soul from the Pit, that he may be enlightened with the light of life.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Pay attention, Job, and listen to me; be silent, and I will speak.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
But if you have something to say, answer me; speak up, for I would like to vindicate you.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
But if not, then listen to me; be quiet, and I will teach you wisdom.”

< Ayuba 33 >