< Ayuba 33 >

1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
Čuj dakle, Jobe, što ću ti kazati, prikloni uho mojim besjedama.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Evo, usta sam svoja otvorio, a jezik riječi pod nepcem mi stvara.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
Iskreno će ti zborit' srce moje, usne će čistu izreći istinu.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
TÓa i mene je duh Božji stvorio, dah Svesilnoga oživio mene.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Ako uzmogneš, ti me opovrgni; spremi se da se suprotstaviš meni!
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Gle, kao i ti, i ja sam pred Bogom, kao i ti, od gline bjeh načinjen;
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
zato ja strahom tebe motrit' neću, ruka te moja neće pritisnuti.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Dakle, na moje uši rekao si - posve sam jasno tvoje čuo riječi:
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
'Nedužan sam i bez ikakva grijeha; prav sam i nema krivice na meni.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Al' On izlike protiv mene traži i za svojeg me drži dušmanina.
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
Noge je moje u klade metnuo, nad svakim mojim on pazi korakom.'
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Ovdje, kažem ti, u pravu ti nisi, jer s Bogom čovjek mjerit' se ne može.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Pa zašto s njime zamećeš prepirku što ti na svaku riječ ne odgovara?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
Bog zbori nama jednom i dva puta, al' čovjek na to pažnju ne obraća.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
U snovima, u viđenjima noćnim, kada san dubok ovlada ljudima i na ležaju dok tvrdo snivaju,
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
tad on govori na uho čovjeku i utvarama plaši ga jezivim
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
da ga od djela njegovih odvrati, da u čovjeku obori oholost,
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
da dušu njegovu spasi od jame i život mu od puta u Podzemlje.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
Bolešću on ga kara na ležaju kad mu se kosti tresu bez prestanka,
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
kad se kruh gadi njegovu životu i ponajbolje jelo duši njegovoj;
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
kada mu tijelo gine naočigled i vide mu se kosti ogoljele,
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
kad mu se duša približava jami a život njegov boravištu mrtvih.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
Ako se uza nj nađe tad anđeo, posrednik jedan između tisuću, da čovjeka na dužnost opomene,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
pa se sažali nad njim i pomoli: 'Izbavi ga da u jamu ne ide; za život njegov nađoh otkupninu!
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
Neka mu tijelo procvate mladošću, nek' se vrati u dane mladenačke!'
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
Vapije k Bogu i Bog ga usliša: radosno On ga pogleda u lice; vrati čovjeku pravednost njegovu.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Tada čovjek pred ljudima zapjeva: 'Griješio sam i pravo izvrtao, ali mi Bog zlom nije uzvratio.
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
On mi je dušu spasio od jame i život mi se veseli svjetlosti.'
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Gle, sve to Bog je spreman učiniti do dva i do tri puta za čovjeka:
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
da dušu njegovu spasi od jame i da mu život svjetlošću obasja.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Pazi dÓe, Jobe, dobro me poslušaj; šuti, jer nisam sve još izrekao.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Ako riječi još imaš, odvrati mi, zbori - rado bih opravdao tebe.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
Ako li nemaš, poslušaj me samo: pazi, rad bih te poučit' mudrosti.”

< Ayuba 33 >