< Ayuba 32 >

1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
Böylece bu üç kişi Eyüp'e yanıt vermekten vazgeçti, çünkü Eyüp kendi doğruluğundan emindi.
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
Ram ailesinden Bûzlu Barakel oğlu Elihu Eyüp'e çok öfkelendi. Çünkü Eyüp kendini Tanrı'dan haklı görüyordu.
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
Elihu Eyüp'ün üç arkadaşına da öfkelendi, çünkü Eyüp'ü suçlamalarına karşın sağlam bir yanıt bulamamışlardı.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
Elihu Eyüp'le konuşmak için sırasını beklemişti, çünkü ötekiler yaşça kendisinden büyüktü.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
Bu üç kişinin başka bir şey söyleyemeyeceğini görünce öfkesi alevlendi.
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
Bûzlu Barakel oğlu Elihu şöyle konuştu: “Ben yaşça küçüğüm, sizse yaşlısınız. Bu yüzden çekindim, bildiğimi söylemekten korktum.
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
‘Çok gün görenler konuşsun’ dedim, ‘Çok yıl yaşayanlar bilgeliği öğretsin.’
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Oysa insana ruh, Her Şeye Gücü Yeten'in soluğu akıl verir.
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
Akıl yaşta değil baştadır. Adaleti anlamak yaşa bakmaz.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
“Bu yüzden, ‘Beni dinleyin’ diyorum, Ben de bildiğimi söyleyeyim.
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
Siz konuşurken ben bekledim, Siz ne diyeceğinizi araştırırken Düşüncelerinizi dinledim.
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
Bütün dikkatimi size çevirdim. Ama hiçbiriniz Eyüp'ün haksızlığını kanıtlayamadı, Onun söylediklerine karşılık veremedi.
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
‘Biz bilgeliğe eriştik, Bırakın Tanrı onu haksız çıkarsın, insan değil’ demeyin.
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
Ama Eyüp'ün sözlerinin hedefi ben değildim, Bu yüzden onu sizin sözlerinizle yanıtlamayacağım.
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
“Onlar yıldı, yanıt veremiyorlar artık, Söyleyecek şeyleri kalmadı.
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
Onlar konuşmuyor diye ben beklemeli miyim, Duruyor, yanıt vermiyorlar diye?
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
Benim de söyleyecek sözüm var, Ben de bildiğimi söyleyeceğim.
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
Çünkü içim dolu, İçimdeki ruh beni zorluyor.
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
İçim açılmamış şarap gibi, Yeni şarap tulumları gibi patlamak üzere.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
Konuşup rahatlamalıyım, Ağzımı açıp yanıtlamalıyım.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
Kimseye ayrıcalık göstermeyecek, Kimseye yaltaklanmayacağım.
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
Çünkü yaltaklanmayı bilsem, Yaratıcım beni hemen yok ederdi.

< Ayuba 32 >