< Ayuba 32 >

1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
Då vände de tre män åter att svara Job; efter han höll sig rättfärdigan.
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
Men Elihu, Baracheels son, af Bus af Kams slägte, vardt vreder uppå Job, att han höll sina själ rättfärdigare än Gud.
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
Ock vardt han vred uppå de tre hans vänner, att de intet svar funno, och dock fördömde Job.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
Ty Elihu hade bidt, så länge de hade talat med Job, efter de voro äldre än han.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
Derföre, då, han såg, att intet svar var i de tre mäns mun, vardt han vred.
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
Och så svarade Elihu, Baracheels son, af Bus, och sade: Jag är ung, och I ären gamle, derföre hafver jag skytt, och fruktat bevisa min konst på eder.
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
Jag tänkte: Låt åren tala, och åldren bevisa vishet.
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Men anden är i menniskone, och dens Allsmägtigas Ande gör henne förståndiga.
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
Mästarena äro icke de visaste, och de gamle förstå icke hvad rätt är.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Derföre vill jag ock tala; hör härtill, jag vill ock bevisa mina konst.
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
Si, jag hafver bidt, medan I talat hafven; jag hafver gifvit akt på edart förstånd, tilldess I hafven gjort en ända på edart tal.
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
Och jag hafver haft akt uppå eder, och si, ingen är ibland eder, som Job straffa, eller till hans ord svara kan.
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
I mågen tilläfventyrs säga: Vi hafve drabbat på vishetena, att Gud hafver bortkastat honom, och ingen annar.
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
Det talet gör mig icke fyllest; jag vill intet svara honom, efter som I taladen.
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
Ack! de uppgifvas, och kunna intet mer svara; de kunna intet mer tala.
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
Efter jag nu bidt hafver, och de kunna intet tala; förty de stå tyste, och svara intet mer;
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
Vill jag dock svara min part, och bevisa mina konst;
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
Ty jag är så full med ordom, att min ande ängslas i minom buk.
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
Si, min buk är såsom must, dem tilltäppt är, hvilken ny fat sönderslår.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
Jag måste tala, att jag må få andas; jag måste upplycka mina läppar och svara.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
Jag vill på ingens person se, och ingo mennisko till vilja tala;
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
Förty jag vet icke, om jag så gjorde, om min skapare innan en kort tid mig borttagandes vorde.

< Ayuba 32 >