< Ayuba 32 >

1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
Então aqueles três homens cessaram de responder a Jó, porque ele era justo em seus olhos.
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
Porém se acendeu a ira de Eliú, filho de Baraquel, buzita, da família de Rão; contra Jó se acendeu sua ira, porque justificava mais a si mesmo que a Deus.
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
Também sua ira se acendeu contra seus três amigos, porque não achavam o que responder, ainda que tinham condenado a Jó.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
E Eliú tinha esperado a Jó naquela discussão, porque tinham mais idade que ele.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
Porém quando Eliú viu que não havia resposta na boca daqueles três homens, sua ira se acendeu.
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
Por isso Eliú, filho de Baraquel, buzita, respondeu, dizendo: Eu sou jovem e vós sois idosos; por isso fiquei receoso e tive medo de vos declarar minha opinião.
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
Eu dizia: Os dias falem, e a multidão de anos ensine sabedoria.
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Certamente há espírito no ser humano, e a inspiração do Todo-Poderoso os faz entendedores.
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
Não são [somente] os grandes que são sábios, nem [somente] os velhos entendem o juízo.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Por isso eu digo: escutai-me; também eu declararei minha opinião.
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
Eis que eu aguardei vossas palavras, [e] dei ouvidos a vossas considerações, enquanto vós buscáveis argumentos.
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
Eu prestei atenção a vós, porém eis que ninguém há de vós que possa convencer a Jó, [nem] que responda a suas palavras.
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
Portanto não digais: Encontramos a sabedoria; que Deus o derrote, [e] não o homem.
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
Jó não dirigiu suas palavras a mim, nem eu lhe responderei com vossos dizeres.
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
Estão pasmos, não respondem mais; faltam-lhes palavras.
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
Esperei, pois, porém [agora] não falam; porque já pararam, [e] não respondem mais.
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
Também eu responderei minha parte; também eu declararei minha opinião.
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
Porque estou cheio de palavras, e o espírito em meu ventre me obriga.
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
Eis que meu ventre é como o vinho que não tem abertura; e que está a ponto de arrebentar como odres novos.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
Falarei, para que eu me alivie; abrirei meus lábios, e responderei.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
Não farei eu acepção de pessoas, nem usarei de títulos lisonjeiros para com o homem.
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
Pois não sei lisonjear; [caso contrário], meu Criador logo me removeria.

< Ayuba 32 >