< Ayuba 32 >
1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
De tre menn svarte ikke Job mere, fordi han var rettferdig i sine egne øine.
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
Da optendtes Elihus vrede - han stammet fra Bus og var sønn av Barak'el, av Rams ætt. Mot Job optendtes hans vrede, fordi han holdt sig selv for å være rettferdig for Gud,
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
og mot hans tre venner optendtes hans vrede, fordi de ikke fant noget svar og allikevel dømte Job skyldig.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
Elihu hadde ventet med å tale til Job, fordi de andre var eldre av år enn han.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
Da nu Elihu så at det ikke var noget svar i de tre menns munn, da optendtes hans vrede.
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
Så tok da Elihu, sønn av Barak'el, busitten, til orde og sa: Jeg er ung av år, og I er gråhårede; derfor holdt jeg mig tilbake og torde ikke uttale for eder hvad jeg vet.
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
Jeg tenkte: La alderen tale og de mange år forkynne visdom!
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Dog, det er menneskets ånd og den Allmektiges åndepust som gjør forstandig.
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
De gamle er ikke alltid vise, ikke alltid forstår oldinger hvad rett er.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Derfor sier jeg: Hør nu på mig! Også jeg vil uttale hvad jeg vet.
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
Jeg ventet på eders ord, jeg lyttet efter forstandig tale fra eder, mens I grundet på hvad I skulde si.
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
Jeg gav akt på eder; men det var ingen av eder som gjendrev Job, ingen som svarte på hans ord.
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
Si ikke: Vi har funnet visdom hos ham; bare Gud kan få bukt med ham, ikke noget menneske!
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
Han har jo ikke rettet sin tale mot mig, og med eders ord vil jeg ikke svare ham.
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
De er forferdet og svarer ikke mere; ordene er blitt borte for dem.
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
Skal jeg vente, fordi de ikke taler, fordi de står der og ikke svarer mere?
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
Også jeg vil nu svare for min del; også jeg vil uttale hvad jeg vet.
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
For jeg er full av ord; ånden i mitt indre driver mig.
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
Mitt indre er som innestengt vin; som nyfylte skinnsekker vil det revne.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
Jeg vil tale, så jeg kan få luft; jeg vil åpne mine leber og svare.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
Jeg vil ikke ta parti for nogen, og jeg vil ikke smigre for noget menneske;
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
for jeg forstår ikke å smigre; ellers kunde min skaper lett rykke mig bort.