< Ayuba 32 >
1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
Omiserunt autem tres viri isti respondere Iob, eo quod iustus sibi videretur.
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
Et iratus, indignatusque est Eliu filius Barachel Buzites, de cognatione Ram: iratus est autem adversum Iob, eo quod iustum se esse diceret coram Deo.
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
Porro adversum amicos eius indignatus est, eo quod non invenissent responsionem rationabilem, sed tantummodo condemnassent Iob.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
Igitur Eliu expectavit Iob loquentem: eo quod seniores essent qui loquebantur.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
Cum autem vidisset quod tres respondere non potuissent, iratus est vehementer.
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
Respondensque Eliu filius Barachel Buzites, dixit: Iunior sum tempore, vos autem antiquiores, idcirco demisso capite, veritus sum vobis indicare meam sententiam.
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
Sperabam enim quod aetas prolixior loqueretur, et annorum multitudo doceret sapientiam.
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Sed, ut video, Spiritus est in hominibus, et inspiratio Omnipotentis dat intelligentiam.
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
Non sunt longaevi sapientes, nec senes intelligunt iudicium.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Ideo dicam: Audite me, ostendam vobis etiam ego meam sapientiam.
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
Expectavi enim sermones vestros, audivi prudentiam vestram, donec disceptaremini sermonibus:
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
Et donec putabam vos aliquid dicere, considerabam: sed, ut video, non est qui possit arguere Iob, et respondere ex vobis sermonibus eius.
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
Ne forte dicatis: Invenimus sapientiam, Deus proiecit eum, non homo.
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
Nihil locutus est mihi, et ego non secundum sermones vestros respondebo illi.
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
Extimuerunt, nec responderunt ultra, abstuleruntque a se eloquia.
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
Quoniam igitur expectavi, et non sunt locuti: steterunt, nec ultra responderunt:
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
Respondebo et ego partem meam, et ostendam scientiam meam.
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
Plenus sum enim sermonibus, et coarctat me spiritus uteri mei.
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
En venter meus quasi mustum absque spiraculo, quod lagunculas novas disrumpit.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
Loquar, et respirabo paululum: aperiam labia mea, et respondebo.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
Non accipiam personam viri, et Deum homini non aequabo.
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
Nescio enim quamdiu subsistam, et si post modicum tollat me Factor meus.