< Ayuba 32 >
1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
Da hörten die drei Männer auf, dem Job noch weiter zu erwidern, obwohl er selbst sich für gerecht erachtete.
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
Auf dieses hin geriet in Zorn Elihu, der Sohn des Barachel aus Buz, von Rams Geschlechte. Er wurde über Job sehr aufgebracht, weil er sich gegenüber Gott für ganz gerecht erachtete.
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
Auch über die drei Freunde ward er zornig, weil sie die rechte Antwort nicht gefunden und Job ins Unrecht setzten.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
Elihu aber hatte nur bei Job gewartet, solange jene redeten, weil sie betagter als er waren.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
Elihu merkte nun, daß diese drei nichts weiter zu erwidern wußten, und so entbrannte mächtig stark sein Zorn.
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
Nun hob Elihu an, der Sohn des Barachel aus Buz, und sprach: "Ich bin noch jung an Jahren; aber ihr seid Greise; ich war daher zu schüchtern und scheute mich, bei euch mein Wissen anzubringen.
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
Ich dachte: Mag das Alter reden, der Jahre Fülle Weisheit lehren!
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Allein der Geist im Menschen ist's, der Odem des Allmächtigen, der sie verständig macht.
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
Nicht die Betagten sind die Weisesten; noch wissen Greise immer, was das Rechte ist.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Drum sage ich: Hört doch auf mich! Ich möchte kundtun, was ich selber weiß.
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
Als ich auf eure Rede wartete, da überlegt ich mir eure Beweise. Bis euch die rechten Worte kämen,
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
solange habe über euch ich nachgedacht. Doch keiner von euch überzeugte Job und widerlegte seine Reden.
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
Sagt nicht: 'Wir fanden Weisheit. Nur Gott vermag ihn zu besiegen, nicht ein Mensch!'
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
Nach meiner Ansicht trug er keine treffenden Beweise vor; ich will ihm nicht erwidern mit Worten gleich den eurigen.
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
Sie sind besiegt, antworten nimmer; sie schoben von sich die Beweise.
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
So fange ich denn an, weil sie nicht reden, dieweil sie dastehn ohne jegliche Erwiderung.
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
Ich möchte gleichfalls meine Lehre künden und kundtun, was ich selber weiß.
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
Denn ich bin voll von Worten; mich drängt der Geist in meinem Innern.
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
Mein Inn'res ist wie festverschlossener Wein, der in den neuen Schläuchen Luft sich macht.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
Ich rede, um mir Luft zu machen, tu meine Lippen auf und spreche.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
Für keinen Menschen nehme ich Partei und nenne niemandem zulieb die Dinge anders,
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
weil ich es nicht verstehe, die Dinge anders zu benennen. Sonst würde kaum mein Schöpfer mich ertragen."