< Ayuba 32 >
1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
Et les trois amis de Job s'abstinrent de lui répondre; car Job était juste devant eux.
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
Et Elihou, fils de Barachiel le Buzite, de la famille de Ram en la terre de Hus, se courrouça; il entra contre Job dans une violente colère, parce qu'il s'était présenté comme juste devant le Seigneur.
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
Et il ne fut pas moins irrité contre les trois amis, parce qu'ils ne pouvaient répondre rien qui confondit Job après l'avoir jugé coupable.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
Et Elihou hésitait à répliquer à Job, car les trois hommes étaient plus avancés que lui en âge.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
Mais lorsqu'il vit que nulle réponse ne sortait de leur bouche, il s'emporta;
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
Et prenant la parole, il dit: Je suis le plus jeune, vous êtes mes anciens; j'ai donc gardé le silence, craignant de vous déclarer ce que je sais,
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
Et je me suis dit: Il n'est point temps de parler; c'est le nombre des années qui donne la sagesse.
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Mais l'esprit réside parmi les mortels et le souffle du Tout-Puissant seul les instruit.
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
Les anciens ne sont point sages, les vieillards ne savent point juger.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Aussi je me décide; écoutez-moi et je vais vous déclarer ce que je sais.
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
Soyez attentifs, je ne cesserai pas que vous n'ayez apprécié mes raisons,
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
Et que je ne sois d'accord avec vous; je n'ai point fait de reproches à Job; celui qui le réfutait était l'un de vous.
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
Je ne voulais pas vous donner occasion de dire: Nous sommes attachés au Seigneur et nous avons trouvé la sagesse.
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
Et vous avez permis à cet homme de tenir un pareil langage!
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
Ils ont été frappés de stupeur; ils n'ont rien trouvé à répondre; ils ont annulé leurs propres arguments.
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
J'ai attendu; je n'ai dit mot; je les ai vus demeurer immobiles sans répliquer.
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
Et Elihou, continuant, s'écria: Eh bien! je parlerai.
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
Car je suis plein de mon sujet; l'esprit en mon sein me consume.
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
Ma poitrine est comme une outre où fermente du vin nouveau; elle ressemble à un soufflet de forge qui éclate.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
Je parlerai tant que mes lèvres pourront s'ouvrir.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
Il n'est point d'homme devant qui j'aie la moindre timidité; il n'est point de mortel qui m'émeuve;
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
Il n'est point de front qui m'impose; s'il en est, que les vers me dévorent.