< Ayuba 32 >

1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
So these three men ceased to respond to Job, because, he, was righteous in their eyes.
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
Then was kindled the anger of Elihu, son of Barachel the Buzite of the family of Ram, —against Job, was kindled his anger, because he justified his own soul rather than God;
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
and, against his three friends, was kindled his anger, —because that they found not a response, and condemned God.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
But, Elihu, had waited for Job with words, because the others were older than he.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
Howbeit, when Elihu saw that there was no response in the mouth of the three men, then was kindled his anger.
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
So then Elihu, son of Barachel, the Buzite, responded and said: —Young, am I, whereas, ye, are aged, For this cause, I faltered, and feared—to shew my knowledge unto you:
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
I said, Days, should speak, —and, the multitude of years, should make known wisdom.
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Yet surely, there is a spirit in men, and, the inspiration of the Almighty, giveth them understanding;
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
Great men, may not be wise, nor, elders, understand justice.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Therefore, I said, Hearken unto me, I will show my knowledge—even I.
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
Lo! I waited for your words, I kept giving ear for your reasons, until ye should search out what to say;
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
Yea, unto you, gave I diligent heed, —But lo! there was, for Job, nothing to convince, nor could you of you answer his speeches.
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
Lest ye should say, We have found out wisdom. GOD, must put him to flight, not man.
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
Since he directed not to me discourse, therefore, with your speeches, will I not reply to him.
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
They were dismayed, they responded no more, they suffered speech to forsake them;
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
Though I waited, yet could they not speak, Surely they came to a stand, they responded no more.
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
I will respond, even I—on my part, I will shew my knowledge, even I!
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
For I am full of discourse, The spirit in my bosom, presseth me on.
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
Lo! my bosom, is like wine not opened, Like new wine-skins, it will burst.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
I will speak, that I may freely breathe, I will open my lips and respond.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
Let me be partial to no man, and, unto no son of earth, give flattering titles,
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
Surely I know not how to give flattering titles, How soon might my Maker take me away!

< Ayuba 32 >