< Ayuba 32 >
1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
And these three men cease from answering Job, for he [is] righteous in his own eyes,
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
and the anger of Elihu son of Barachel the Buzite burns, of the family of Ram; his anger has burned against Job, because of his justifying himself more than God;
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
and his anger has burned against his three friends, because that they have not found an answer, and condemn Job.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
And Elihu has waited earnestly beside Job with words, for they are older than he in days.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
And Elihu sees that there is no answer in the mouth of the three men, and his anger burns.
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
And Elihu son of Barachel the Buzite answers and says: “I [am] young in days, and you [are] aged; Therefore I have feared, And am afraid of showing you my opinion.
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
I said, Days speak, And a multitude of years teach wisdom.
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Surely a spirit is in man, And the breath of the Mighty One Causes them to understand.
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
The multitude are not wise, Nor do the aged understand judgment.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Therefore I have said: Listen to me, I show my opinion—even I.
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
Behold, I have waited for your words, I give ear to your reasons, Until you search out sayings.
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
And to you I attend, And behold, there is no reasoner for Job, [Or] answerer of his sayings among you.
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
Lest you say, We have found wisdom, God thrusts him away, not man.
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
And he has not set words in array for me, And I do not answer him with your sayings.
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
(They have broken down, They have not answered again, They removed words from themselves.
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
And I have waited, but they do not speak, For they have stood still, They have not answered anymore.)
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
I answer, even I—my share, I show my opinion—even I.
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
For I have been full of words, The spirit of my breast has distressed me,
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
Behold, my breast [is] as wine not opened, It is broken up like new bottles.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
I speak, and there is refreshment to me, I open my lips and answer.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
Please do not let me accept the face of any, Nor give flattering titles to man,
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
For I have not known to give flattering titles, My Maker takes me away in a little.”