< Ayuba 32 >

1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
So these three men stopped answering Job, because he was righteous in his own eyes.
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
This kindled the anger of Elihu son of Barachel the Buzite, of the family of Ram. He burned with anger against Job for justifying himself rather than God,
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
and he burned with anger against Job’s three friends because they had failed to refute Job, and yet had condemned him.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
Now Elihu had waited to speak to Job because the others were older than he.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
But when he saw that the three men had no further reply, his anger was kindled.
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
So Elihu son of Barachel the Buzite declared: “I am young in years, while you are old; that is why I was timid and afraid to tell you what I know.
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
I thought that age should speak, and many years should teach wisdom.
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
But there is a spirit in a man, the breath of the Almighty, that gives him understanding.
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
It is not only the old who are wise, or the elderly who understand justice.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Therefore I say, ‘Listen to me; I too will declare what I know.’
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
Indeed, I waited while you spoke; I listened to your reasoning; as you searched for words,
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
I paid you full attention. But no one proved Job wrong; not one of you rebutted his arguments.
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
So do not claim, ‘We have found wisdom; let God, not man, refute him.’
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
But Job has not directed his words against me, and I will not answer him with your arguments.
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
Job’s friends are dismayed, with no more to say; words have escaped them.
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
Must I wait, now that they are silent, now that they stand and no longer reply?
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
I too will answer; yes, I will declare what I know.
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
For I am full of words, and my spirit within me compels me.
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
Behold, my belly is like unvented wine; it is about to burst like a new wineskin.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
I must speak and find relief; I must open my lips and respond.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
I will be partial to no one, nor will I flatter any man.
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
For I do not know how to flatter, or my Maker would remove me in an instant.

< Ayuba 32 >