< Ayuba 32 >

1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
Da lode disse tre Mænd af at svare Job, efterdi han var retfærdig i sine egne Øjne.
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
Men Vreden optændtes hos Elihu, Busiten, Barakels Søn, af Rams Slægt, hans Vrede optændtes imod Job, fordi han vilde holde sin Sjæl retfærdig over for Gud.
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
Hans Vrede optændtes ogsaa imod hans tre Venner, fordi de ikke fandt paa noget Svar og alligevel holdt Job for ugudelig.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
Men Elihu havde biet efter, at Job skulde ende sine Ord; thi hine vare ældre af Aar end han.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
Der Elihu saa, at der var intet Svar i de tre Mænds Mund, da optændtes hans Vrede.
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
Saa svarede Elihu, Busiten, Barakels Søn, og sagde: Jeg er ung af Aar, men I ere bedagede Mænd; derfor undsaa jeg mig og frygtede for at kundgøre eder min Kundskab.
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
Jeg sagde: Lad Dagene tale, og Aars Mangfoldighed kundgøre Visdom!
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Sandelig, det er Aanden i Mennesket og den Almægtiges Aande, som gør ham forstandig.
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
De alderstegne ere ikke altid vise, ej heller forstaa de gamle altid Retten.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Derfor siger jeg: Hør paa mig; ogsaa jeg vil kundgøre min Kundskab.
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
Se, jeg biede efter eders Ord, jeg vendte mine Øren til eders forstandige Tale, indtil I kunde faa udgrundet, hvad I vilde tale.
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
Og jeg har agtet nøje paa eder, men se, der var ingen af eder, som gendrev Job, og som kunde svare paa hans Tale,
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
at I ikke skulde sige: Vi have fundet Visdom; Gud, men ikke et Menneske, kan fælde ham.
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
Men imod mig har han ikke stillet sin Tale, og med eders Ord vil jeg ikke give ham Svar.
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
De ere blevne forskrækkede, de kunne ikke svare mere, borte ere Ordene for dem.
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
Og jeg biede, thi de talte ikke; ja, de stode der, de svarede ikke mere.
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
Nu vil jeg ogsaa svare for min Del, ogsaa jeg vil kundgøre min Kundskab.
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
Thi jeg er fuld af Taler; Aanden i mit Indre trænger paa.
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
Se, mit Indre er som Vin, for hvilken der ikke er aabnet, det maa sprænges som nye Læderflasker.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
Jeg maa tale, at jeg kan faa Luft, jeg maa oplade mine Læber og svare.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
Ikke vil jeg anse nogens Person, og jeg vil ikke smigre for noget Menneske;
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
thi jeg forstaar ikke at smigre; lettelig vilde min Skaber rive mig bort.

< Ayuba 32 >