< Ayuba 32 >

1 Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
Ona tri čovjeka prestadoše Jobu odgovarati, jer je on sebe smatrao nevinim.
2 Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
Nato se rasrdi Elihu, sin Barakeelov, iz Buza, od plemena Ramova: planu gnjevom na Joba zato što je sebe držao pravednim pred Bogom;
3 Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
a planu gnjevom i na tri njegova prijatelja jer nisu više našli ništa što bi odgovorili te su tako Boga osudili.
4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
Dok su oni govorili s Jobom, Elihu je šutio, jer su oni bili stariji od njega.
5 Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
Ali kad vidje da ona tri čovjeka nisu više imala odgovora u ustima, planu od srdžbe.
6 Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
I progovorivši, Elihu, sin Barakeelov, iz Buza, reče: “Po godinama svojim još mlad sam ja, a u duboku vi ste ušli starost; bojažljivo se zato ja ustezah znanje svoje pokazati pred vama.
7 Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
Mišljah u sebi: 'Govorit će starost, mnoge godine pokazat će mudrost.'
8 Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Uistinu, dah neki u ljudima, duh Svesilnog mudrim čini čovjeka.
9 Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
Dob poodmakla ne daje mudrosti a niti starost pravednosti uči.
10 “Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Zato vas molim, poslušajte mene da vam i ja znanje svoje izložim.
11 Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
S pažnjom sam vaše besjede pratio i razloge sam vaše saslušao dok ste tražili što ćete kazati.
12 na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
Na vama moja sva bijaše pažnja, al' ne bi nikog da Joba pobije ni da mu od vas tko riječ opovrgne.
13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
Nemojte reći: 'Na mudrost smo naišli! Bog će ga pobit jer čovjek ne može.'
14 Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
Nije meni on besjedu upravio: odvratit mu neću vašim riječima.
15 “Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
Poraženi, otpovrgnut ne mogu, riječi zapeše u grlu njihovu.
16 Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
Čekao sam! Al', gle, oni ne zbore. Umukoše, ni riječ više da kažu!
17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
Na meni je da progovorim sada, znanje ću svoje i ja izložiti.
18 Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
Riječi mnoge u meni naviru dok iznutra moj duh mene nagoni.
19 a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
Gle, nutrina mi je k'o mošt zatvoren, k'o nova će se raspući mješina.
20 Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
Da mi odlane, govorit ću stoga, otvorit ću usne i odvratit' vama.
21 Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
Nijednoj strani priklonit se neću niti laskat ja namjeravam kome.
22 gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
Laskati ja ne umijem nikako, jer smjesta bi me Tvorac moj smaknuo.

< Ayuba 32 >