< Ayuba 31 >
1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
Hice un pacto con mis ojos. ¿Cómo podría entonces fijar mi mirada en una doncella?
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
¿Cuál sería la recompensa de ʼEloah desde arriba o la herencia de ʼEL-Shadday desde las alturas?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
¿No es la calamidad para el perverso, y el desastre para los que obran iniquidad?
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
¿No observa Él mis caminos y cuenta todos mis pasos?
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
Si anduve con vanidad y mi pie se apresuró al engaño,
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
sea yo pesado en balanza justa, y conozca ʼEloah a mi integridad.
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
Si mi paso se apartó del camino, mi corazón se fue tras mis ojos o si alguna mancha se pegó a mis manos,
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
siembre yo y coma otro. Sea arrancada mi cosecha.
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
Si mi corazón fue seducido por una mujer y aceché a la puerta de mi prójimo,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
muela mi esposa para otro y sobre ella se encorven otros.
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
Porque eso sería una lujuriosa perversidad y una iniquidad castigada por los jueces,
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
un fuego que consume hasta el Abadón, que arrancaría toda mi hacienda.
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
Si menosprecié el derecho de mi esclavo o de mi esclava, cuando ellos tenían una queja contra mí,
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
¿qué haré cuando ʼEL me levante? ¿Qué le responderé cuando me llame a cuentas?
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
El que me formó en el vientre, ¿no lo formó también a él? ¿No nos formó el mismo en la matriz?
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
Si estorbé el anhelo de los pobres o hice desfallecer los ojos de la viuda,
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
o comí mi bocado a solas y el huérfano no comió de él,
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
aunque desde mi juventud creció conmigo como con un padre y lo guié desde el seno materno,
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
si vi a algún vagabundo sin ropas o algún menesteroso sin algo con lo cual cubrirse,
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
y sus órganos internos no me bendijeron al calentarse con el vellón de mis ovejas,
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
si alcé mi mano contra el huérfano cuando me vi apoyado en la puerta,
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
despréndase mi brazo del hombro y descoyúntese mi brazo de su hueso.
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
Porque temo el castigo de ʼEL, pues ante su majestad nada puedo hacer.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
Si fijé mi confianza en el oro y al metal precioso dije: Tú eres mi esperanza,
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
si me complací por mis grandes riquezas y porque mi mano ganó mucho,
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
si miré al sol resplandeciente o a la luna que se desplazaba en su esplendor,
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
si mi corazón fue seducido en secreto y mi boca les envió un beso con la mano,
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
también sería iniquidad digna de castigo, por negar al ʼEL que está en lo alto.
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
¿Me alegré de la ruina del que me aborrecía o salté de júbilo porque el mal cayó sobre él?
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
¡No! Nunca dejé que mi boca pecara, ni al maldecir al enemigo, ni al hacer una imprecación para que muriera.
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
Decían los esclavos de mi casa: ¿Quién no se sació con su carne?
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
El forastero no pasaba la noche en la calle. Yo abría mis puertas al viajero.
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
Si encubrí mis transgresiones como Adán y oculté la iniquidad en mi seno
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
por temor a la muchedumbre, o porque el desprecio de la gente me intimidó y no salí a la puerta.
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
¡Ojalá me escuchara! ¡Ciertamente aquí está mi firma! ¡Que ʼEL-Shadday me responda!
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
Ciertamente lo llevaría sobre mi hombro y me lo ataría a la cabeza como una corona.
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
Le rendiría cuenta de todos mis pasos, y como a un príncipe me acercaría ante Él.
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
Si mi tierra clama contra mí y lloran sus surcos junto a ella,
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
si comí su fruto sin pagar o afligí a sus labradores,
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
crezcan abrojos en lugar de trigo y cizaña en vez de cebada. Aquí terminan las palabras de Job.