< Ayuba 31 >

1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
“Me prometí a mí mismo no mirar nunca con deseo a las jóvenes.
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
¿Qué debe esperar la gente de Dios? ¿Qué recompensa debe darles el Todopoderoso en lo alto?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
¿No es el desastre para los malvados y la destrucción para los que hacen el mal?
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
¿No ve Dios todo lo que hago, incluso cuenta cada paso que doy?
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
¿He vivido una vida engañosa? ¿He estado ansioso por decir mentiras?
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
¡No! Que Dios me pese en la balanza de su justicia y que descubra mi integridad.
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
“Si me he desviado del camino de Dios, si he dejado que lo que veo se convierta en mis deseos, si hay alguna mancha de pecado en mis manos,
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
entonces que otro coma lo que he sembrado, y que todo lo que he cultivado sea desarraigado.
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
Si una mujer me ha seducido, o si he buscado la oportunidad de acostarme con la mujer de mi prójimo,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
que mi esposa sirva a otro, que otros hombres se acuesten con ella.
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
Porque eso sería una maldad, un pecado que merece castigo,
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
porque este pecado es como un fuego que lleva a la destrucción, destruyendo todo lo que tengo.
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
“Si me negara a escuchar a mis siervos o siervas cuando me trajeran sus quejas,
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
¿qué haría cuando Dios viniera a juzgarme? ¿Cómo respondería si me investigara?
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
¿Acaso el mismo Dios no nos hizo a todos?
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
¿Me he negado a dar a los pobres lo que necesitaban, o he hecho desesperar a las viudas?
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
¿Acaso he comido yo solo un trozo de pan? ¿No he compartido siempre mi comida con los huérfanos?
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
Desde que era joven fui padre de los huérfanos y cuidé de las viudas.
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
Si alguna vez veía a alguien necesitado de ropa, a los pobres sin nada que ponerse,
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
siempre me agradecían la ropa de lana que los mantenía calientes.
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
“Si levantaba la mano para golpear a un huérfano, seguro de que si llegaba a los tribunales los jueces estarían de mi parte,
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
entonces que mi hombro sea arrancado de su articulación, que mi brazo sea arrancado de su cavidad.
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
Como me aterra el castigo que Dios me tiene reservado, y debido a su majestad, nunca podría hacer esto.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
“¿He puesto mi confianza en el oro, llamando al oro fino ‘mi seguridad’?
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
¿Me he deleitado en ser rico, feliz por todas mis riquezas que había ganado?
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
¿He mirado el sol brillando tan intensamente o la luna moviéndose con majestuosidad por el cielo
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
y he tenido la tentación de adorarlos secretamente besando mi mano ante ellos como señal de devoción?
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
Esto también sería un pecado que merece castigo porque significaría que he negado a Dios en lo alto.
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
“¿Alguna vez me he alegrado cuando el desastre destruyó a los que me odiaban, o he celebrado cuando el mal los derribó?
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
Nunca he permitido que mi boca pecara echando una maldición sobre la vida de alguien.
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
¿No ha preguntado mi familia: ‘¿Hay alguien que no haya comido todo lo que quería de su comida?’
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
Nunca he dejado dormir a extraños en la calle; he abierto mis puertas a los viajeros.
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
¿He ocultado mis pecados a los demás, escondiendo mi maldad en lo más profundo de mí?
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
¿Tenía miedo de lo que pensaran los demás, del desprecio que me hicieran las familias, y por eso me callaba y no salía?
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
“¿Por qué nadie escucha lo que digo? Firmo con mi nombre para avalar todo lo que he dicho. Que el Todopoderoso me responda. Que mi acusador escriba de qué me acusa.
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
Yo los pondría en alto; Los llevaría en mi cabeza como una corona.
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
Le explicaría todo lo que había hecho; mantendría la cabeza alta ante él.
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
“Si mi tierra ha gritado contra mí; si sus surcos han llorado por mí;
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
si he tomado sus cosechas sin pago o si he causado daño a los agricultores;
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
entonces que crezcan espinas en lugar de trigo, y cizaña en lugar de cebada”. Las palabras de Job se terminan.

< Ayuba 31 >