< Ayuba 31 >

1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
با چشمان خود عهد بستم که هرگز با نظر شهوت به دختری نگاه نکنم.
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
خدای قادر مطلق که در بالاست برای ما چه تدارک دیده است؟
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
آیا مصیبت و بلا سرنوشت شریران و بدکاران نیست؟
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
آیا او هر کاری را که می‌کنم و هر قدمی را که برمی‌دارم نمی‌بیند.
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
من هرگز دروغ نگفته و کسی را فریب نداده‌ام.
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
بگذار خدا خودش مرا با ترازوی عدل بسنجد و ببیند که بی‌گناهم.
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
اگر پایم را از راه خدا بیرون گذاشته‌ام، یا اگر دلم در طمع چیزهایی بوده که چشمانم دیده است، یا اگر دستهایم به گناه آلوده شده است،
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
باشد که غله‌ای که کاشته‌ام از ریشه کنده شود و یا شخص دیگری آن را درو کند.
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
اگر شیفتهٔ زن مرد دیگری شده، در کمین او نشسته‌ام،
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
باشد که همسرم را مرد دیگری تصاحب کند؛
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
زیرا این کار زشت سزاوار مجازات است،
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
و مانند آتشی جهنمی می‌تواند تمام هستی مرا بسوزاند و از بین ببرد.
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
اگر نسبت به غلام یا کنیز خود بی‌انصافی می‌کردم، وقتی که از من شکایت داشتند،
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
چگونه می‌توانستم با خدا روبرو شوم؟ و هنگامی که در این باره از من سؤال می‌کرد، چه جوابی می‌دادم؟
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
چون هم من و هم خدمتگزارانم، به دست یک خدا سرشته شده‌ایم.
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
هرگز از کمک کردن به فقرا کوتاهی نکرده‌ام. هرگز نگذاشته‌ام بیوه‌زنی در ناامیدی بماند،
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
یا یتیمی گرسنگی بکشد، بلکه خوراک خود را با آنها قسمت کرده‌ام
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
و تمام عمر خود را صرف نگهداری از آنها نموده‌ام.
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
اگر کسی را می‌دیدم که لباس ندارد و از سرما می‌لرزد،
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
لباسی از پشم گوسفندانم به او می‌دادم تا از سرما در امان بماند و او با تمام وجود برای من دعای خیر می‌کرد.
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
اگر من با استفاده از نفوذی که در دادگاه داشته‌ام حق یتیمی را پایمال نموده باشم
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
بازویم از کتفم بیفتد و دستم بشکند.
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
هرگز جرأت نمی‌کردم چنین کاری را انجام دهم، زیرا از مجازات و عظمت خدا می‌ترسیدم.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
هرگز به طلا و نقره تکیه نکرده‌ام
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
و شادی من متکی به مال و ثروت نبوده است.
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
هرگز فریفتهٔ خورشید تابان و ماه درخشان نشده‌ام و آنها را از دور نبوسیده و پرستش نکرده‌ام؛
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
چون اگر مرتکب چنین کارهایی شده بودم مفهومش این بود که خدای متعال را انکار کرده‌ام، و چنین گناهی بی‌سزا نمی‌ماند.
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
هرگز از مصیبت دشمن شادی نکرده‌ام،
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
هرگز آنها را نفرین نکرده‌ام و زبانم را از این گناه باز داشته‌ام.
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
هرگز نگذاشته‌ام خدمتگزارانم گرسنه بمانند.
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
هرگز نگذاشته‌ام غریبه‌ای شب را در کوچه بخوابد، بلکه در خانهٔ خود را به روی او باز گذاشته‌ام.
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
هرگز مانند دیگران به خاطر ترس از سرزنش مردم، سعی نکرده‌ام گناهانم را پنهان سازم و خاموش در داخل خانهٔ خود بنشینم.
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
ای کاش کسی پیدا می‌شد که به حرفهایم گوش بدهد! من دفاعیهٔ خود را تقدیم می‌کنم. بگذار قادر مطلق جواب مرا بدهد و اتهاماتی را که به من نسبت داده شده به من نشان دهد،
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
و من آنها را مانند تاجی بر سر می‌گذارم!
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
تمام کارهایی را که کرده‌ام برای او تعریف می‌کنم و سربلند در حضور او می‌ایستم.
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
اگر زمینی که در آن کشت می‌کنم مرا متهم سازد به اینکه صاحبش را کشته‌ام و آن را تصاحب کرده‌ام تا از محصولش استفاده برم،
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
باشد که در آن زمین به جای گندم، خار و به عوض جو، علفهای هرز بروید. پایان سخنان ایوب.

< Ayuba 31 >