< Ayuba 31 >

1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
Pepigi fœdus cum oculis meis, ut ne cogitarem quidem de virgine.
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
Quam enim partem haberet in me Deus desuper, et hæreditatem Omnipotens de excelsis?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
Numquid non perditio est iniquo, et alienatio operantibus injustitiam?
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
Nonne ipse considerat vias meas, et cunctos gressus meos dinumerat?
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
Si ambulavi in vanitate, et festinavit in dolo pes meus,
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
appendat me in statera justa, et sciat Deus simplicitatem meam.
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
Si declinavit gressus meus de via, et si secutum est oculos meos cor meum, et si manibus meis adhæsit macula,
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
seram, et alius comedat, et progenies mea eradicetur.
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
Si deceptum est cor meum super muliere, et si ad ostium amici mei insidiatus sum,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
scortum alterius sit uxor mea, et super illam incurventur alii.
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
Hoc enim nefas est, et iniquitas maxima.
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
Ignis est usque ad perditionem devorans, et omnia eradicans genimina.
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
Si contempsi subire judicium cum servo meo et ancilla mea, cum disceptarent adversum me:
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
quid enim faciam cum surrexerit ad judicandum Deus? et cum quæsierit, quid respondebo illi?
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
Numquid non in utero fecit me, qui et illum operatus est, et formavit me in vulva unus?
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
Si negavi quod volebant pauperibus, et oculos viduæ expectare feci;
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
si comedi buccellam meam solus, et non comedit pupillus ex ea
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
(quia ab infantia mea crevit mecum miseratio, et de utero matris meæ egressa est mecum);
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
si despexi pereuntem, eo quod non habuerit indumentum, et absque operimento pauperem;
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
si non benedixerunt mihi latera ejus, et de velleribus ovium mearum calefactus est;
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
si levavi super pupillum manum meam, etiam cum viderem me in porta superiorem:
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
humerus meus a junctura sua cadat, et brachium meum cum suis ossibus confringatur.
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
Semper enim quasi tumentes super me fluctus timui Deum, et pondus ejus ferre non potui.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
Si putavi aurum robur meum, et obrizo dixi: Fiducia mea;
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
si lætatus sum super multis divitiis meis, et quia plurima reperit manus mea;
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
si vidi solem cum fulgeret, et lunam incedentem clare,
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
et lætatum est in abscondito cor meum, et osculatus sum manum meam ore meo:
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
quæ est iniquitas maxima, et negatio contra Deum altissimum.
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
Si gavisus sum ad ruinam ejus qui me oderat, et exsultavi quod invenisset eum malum:
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
non enim dedi ad peccandum guttur meum, ut expeterem maledicens animam ejus.
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
Si non dixerunt viri tabernaculi mei: Quis det de carnibus ejus, ut saturemur?
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
foris non mansit peregrinus: ostium meum viatori patuit.
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
Si abscondi quasi homo peccatum meum, et celavi in sinu meo iniquitatem meam;
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
si expavi ad multitudinem nimiam, et despectio propinquorum terruit me: et non magis tacui, nec egressus sum ostium.
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
Quis mihi tribuat auditorem, ut desiderium meum audiat Omnipotens, et librum scribat ipse qui judicat,
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
ut in humero meo portem illum, et circumdem illum quasi coronam mihi?
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
Per singulos gradus meos pronuntiabo illum, et quasi principi offeram eum.
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
Si adversum me terra mea clamat, et cum ipsa sulci ejus deflent:
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
si fructus ejus comedi absque pecunia, et animam agricolarum ejus afflixi:
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
pro frumento oriatur mihi tribulus, et pro hordeo spina. Finita sunt verba Job.

< Ayuba 31 >