< Ayuba 31 >
1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
Szövetséget kötöttem szemeimmel, hogyan vetnék hát ügyet hajadonra?
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
Hisz mely osztályrész jut Istentől felülről s mely örökség a Mindenhatótól a magasból?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
Nemde balsors a jogtalannak s viszontagság a gonosztevőknek.
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
Nemde ő látja útaimat s mind a lépéseimet megszámlálja!
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
Ha hamissággal jártam és csalárdságra sietett a lábam –
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
mérjen meg engem igaz serpenyőn s tudja meg Isten gáncstalanságomat –
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
ha léptem elhajolt az útról és szemeim után járt a szívem, kezeimhez hiba tapadt:
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
hadd vessek és más egyék, és sarjaim tépessenek ki gyökerestül!
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
Ha szívem elcsábíttatta magát asszony miatt, felebarátom ajtaján leskelődtem:
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
másnak őröljön a feleségem és mások hajoljanak reá;
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
mert gazság az, s bírák elé való bűn az,
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
mert tűz az, mely az enyészetig emészt, s minden termésemet gyökerestül tépi ki!
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
Ha megvetettem szolgám és szolgálóm jogát, mikor pöröltek velem –
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
hiszen mit teszek majd, midőn Isten fölkel s midőn számon kér, mit felelek neki,
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
hiszen az anyaméhben ki engem alkotott, alkotta őt és Egy formált minket a méhben –
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
ha megvontam a kívántat a szegényektől s az özvegy szemeit epesztettem,
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
s én egyedül ettem falatomat s árva nem evett belőle
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
– hisz ifjúkorom óta nálam nőtt fel, mint atyánál, s mint anyám méhéből valót úgy vezettem -;
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
ha láttam bujdosót öltözet nélkül s takarója nincs a szűkölködőnek,
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
ha nem áldottak engem ágyékai s bárányaim nyíretéből fel nem melegedett;
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
ha fölemeltem kezemet az árvára, midőn a kapuban láttam segítségemet:
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
vállam essék ki a lapoczkájából és törjék el karom a szárából;
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
mert rettenet nekem az Istentől való balsors, s fensége miatt nem tehetném!
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
Ha aranyat tettem bizalmammá és a színaranyat mondtam bizodalmamnak;
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
ha örültem, hogy nagy a vagyonom s hogy sokat ért el kezem;
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
ha láttam a napvilágot, hogy ragyog, s a holdat, a mint dicsőn halad,
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
és szívem elcsábult titokban és kezem csókra nyúlt a szájamhoz:
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
az is bíró elé való bűn, mert megtagadtam volna Istent felülről!
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
Ha örültem gyűlölőm elesésén s felbuzdultam, midőn baj érte –
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
hisz nem engedtem ínyemet, hogy vétkezzen, hogy átokkal kérjem lelkét -;
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
ha nem mondták sátram emberei: bár volna, ki húsából nem lakott jól
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
az utczán nem hált meg jövevény, az út felé tártam ki ajtaimat -;
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
ha emberek módjára takargattam bűntetteimet, keblemre rejtve bűnömet,
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
mert rettegtem a nagy tömegtől s megijesztett a családok gúnyja, úgy hogy csendben voltam, nem mentem ki a kapun!
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
Vajha volna, ki rám hallgatna – íme jegyem, feleljen nekem a Mindenható – és a vádlevél, melyet írt a pörös felem:
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
bizony, vállamon hordanám azt, felfűzném koszorúnak magamra,
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
lépéseim számát bevallanám neki, akár egy fejedelem közeledném hozzá!
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
Ha ellenem kiáltott földem s egyaránt sírtak barázdái;
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
ha erejét emésztettem pénz nélkül és gazdájával kileheltettem lelkét:
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
búza helyett sarjadjon bogáncs, és árpa helyett gazfű! Vége Jób beszédeinek.