< Ayuba 31 >

1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
J'avais fait un pacte avec mes yeux, disant: Je ne regarderai plus une vierge.
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
Car quelle est la part que d'en haut m'a réservée le Seigneur; quel héritage dois-je attendre du Tout-Puissant qui règne au plus haut des cieux?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
Malheur, perdition à l'injuste, expulsion pour celui qui fait le mal.
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
Le Seigneur ne me tiendra-t-il pas compte de mes voies, ni de la manière dont j'ai marché?
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
Si j'avais été le compagnon des railleurs; si j'avais porté mes pas du côté de la fraude!
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
Mais je me suis maintenu sous le joug de la justice, et le Seigneur connaît mon innocence.
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
Si mon pied s'est écarté du droit chemin, si mon cœur a été égayé par mes yeux, si mes mains ont touché des présents,
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
Que d'autres consomment ce que j'ai semé, que sur la terre je devienne sans racines.
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
Si mon cœur a convoité la femme d'autrui, si j'ai franchi ses portes,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
Que ma femme plaise à un autre homme; que mes enfants soient humiliés.
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
Rien ne peut apaiser la colère de Dieu contre celui qui souille la femme de son prochain.
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
Le feu s'attaquera à toute sa personne et dévorera tout ce qui sera issu de lui.
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
Si j'avais faussé le jugement que je rendais sur mon serviteur et ma servante, lorsqu'ils recouraient à ma justice,
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
Que ferais-je quand à mon tour le Seigneur me jugera? Qu'aurais-je à lui répondre, s'il m'avait surpris en quelque faute?
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
Ceux que j'avais à juger n'avaient-ils pas été comme moi, conçus en des entrailles? n'était-ce pas comme si les mêmes flancs nous avaient portés?
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
Aussi les pauvres ont-ils toujours trouvé chez moi ce qui leur manquait; et je n'ai point fait verser de larmes à l'œil de la veuve.
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
Si j'ai mangé seul ma bouchée, si je n'en ai point fait part à l'orphelin;
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
Si dès ma jeunesse, à peine sorti du ventre de ma mère, je n'ai eu de lui des soins paternels;
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
Si j'ai méprisé l'homme nu et abandonné; si je ne l'ai point vêtu;
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
Si les indigents ne m'ont point béni; si leurs épaules n'ont pas été réchauffées par les toisons de mes agneaux;
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
Si j'ai levé la main sur le pupille; si je n'ai point multiplié mes secours avec confiance;
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
Que mon épaule se déboîte, que mon bras soit broyé au-dessous du coude.
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
En vérité la crainte du Seigneur m'a saisi; je ne puis supporter ce qu'il m'envoie.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
Si j'avais amoncelé de l'or, si j'avais estimé surtout les pierres précieuses;
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
Si j'avais mis ma joie en de grandes richesses; si ma main s'était posée sur des trésors innombrables;
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
Je me serais dit: N'ai-je point vu le soleil dans tout son éclat s'éclipser, et la lune au ciel périr? Et rien n'est au-dessus d'eux.
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
Et si mon cœur en secret s'est laissé séduire; et si j'ai baisé ma main en la portant à ma bouche,
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
Que ces fautes me soient gravement imputées; car alors j'ai menti au Seigneur Très-Haut.
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
Et si je me suis réjoui de la chute de mes ennemis, et si dans mon âme j'ai dit: Bien!
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
Puisse mon oreille ouïr la malédiction qui sera portée contre moi; puissé-je être signalé à tout le peuple comme un méchant.
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
Si je n'ai pas été bon pour mes servantes, si elles ont dit de moi: Qui nous permettra de nous rassasier de sa chair?
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
Si j'ai laissé l'étranger passer la nuit en plein air, et si ma porte ne s'est pas ouverte à tout venant.
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
Si ayant failli involontairement, j'ai caché mes péchés;
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
Retenu par la honte de les avouer devant la multitude; si j'ai souffert que le pauvre sortît de ma maison l'estomac vide;
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
Qui me donnera quelqu'un qui m'écoute? Si je n'ai point eu crainte de la main du Seigneur; le titre que j'avais contre autrui,
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
Que j'avais lu les épaules ceintes d'une couronne,
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
Si je ne l'ai point remis, après l'avoir déchiré, sans rien exiger du débiteur;
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
Si jamais la terre a gémi contre moi, si ses sillons ont pleuré tous ensemble,
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
Si j'ai consommé ses fruits seul et sans les payer; si en les empruntant j'ai affligé l'âme de son possesseur,
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
Que les champs, au lieu de froment, ne produisent pour moi que des orties; et au lieu d'orge que des ronces. Et Job cessa de parler.

< Ayuba 31 >