< Ayuba 31 >
1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
"Minä olen tehnyt liiton silmäini kanssa: kuinka voisinkaan katsoa neitosen puoleen!
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
Minkä osan antaisi silloin Jumala ylhäältä, minkä perintöosan Kaikkivaltias korkeudesta?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
Tuleehan väärälle turmio ja onnettomuus väärintekijöille.
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
Eikö hän näkisi minun teitäni ja laskisi kaikkia minun askeleitani?
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
Jos minä ikinä valheessa vaelsin, jos jalkani kiiruhti petokseen,
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
punnitkoon minut Jumala oikealla vaa'alla, ja hän on huomaava minun nuhteettomuuteni.
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
Jos minun askeleeni poikkesivat tieltä ja minun sydämeni seurasi silmiäni tahi tahra tarttui minun käsiini,
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
niin syököön toinen, mitä minä kylvän, ja minun vesani revittäköön juurinensa.
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
Jos minun sydämeni hullaantui toisen vaimoon ja minä väijyin lähimmäiseni ovella,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
niin jauhakoon oma vaimoni vieraalle, ja halailkoot häntä muut;
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
sillä se olisi ollut ilkityö ja raskaasti rangaistava rikos,
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
tuli, joka kuluttaisi manalaan saakka ja hävittäisi kaiken saatuni.
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
Jos minä pidin halpana palvelijani ja palvelijattareni oikeuden, kun heillä oli riita minun kanssani,
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
niin mitä minä tekisin, jos Jumala nousisi, ja mitä vastaisin hänelle, jos hän kävisi tutkimaan?
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
Eikö sama, joka äidin kohdussa loi minut, luonut häntäkin, eikö sama meitä äidin sydämen alla valmistanut?
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
Olenko minä kieltänyt vaivaisilta heidän toivomuksensa ja saattanut lesken silmät sammumaan?
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
Olenko syönyt leipäpalani yksinäni, orvonkin saamatta syödä siitä?
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
En, vaan nuoruudestani saakka minä kasvatin häntä niinkuin oma isä ja äitini kohdusta asti minä holhosin häntä.
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
Jos minä näin menehtyväisen vaatteetonna ja köyhän verhoa vailla,
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
jos hänen lanteensa eivät minua siunanneet eikä hän saanut lämmitellä minun karitsaini villoilla,
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
jos minä puin nyrkkiä orvolle, kun näin puoltani pidettävän portissa,
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
niin irtautukoon olkapääni hartiastani, ja murtukoon käsivarteni sijoiltansa.
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
Sillä silloin olisi minun peljättävä turmiota Jumalalta, enkä kestäisi hänen valtasuuruutensa edessä.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
Jos minä panin uskallukseni kultaan ja sanoin hienolle kullalle: 'Sinä olet minun turvani',
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
jos iloitsin siitä, että rikkauteni oli suuri ja että käteni oli saanut paljon hankituksi,
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
jos katsellessani aurinkoa, kuinka se loisti, ja kuuta, joka ylhänä vaelsi,
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
sydämeni antautui salaa vieteltäväksi ja käteni niille suudelmia heitti,
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
niin olisi sekin raskaasti rangaistava rikos, sillä minä olisin kieltänyt korkeuden Jumalan.
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
Olenko iloinnut vihamieheni vahingosta, riemusta hykähtänyt, kun häntä onnettomuus kohtasi?
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
En ole sallinut suuni syntiä tehdä, kiroten vaatia hänen henkeänsä.
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
Eikö täydy minun talonväkeni myöntää, että kukin on saanut lihaa yllin kyllin?
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
Muukalaisen ei tarvinnut yötä ulkona viettää; minä pidin oveni auki tielle päin.
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
Olenko ihmisten tavoin peitellyt rikkomuksiani, kätkenyt poveeni pahat tekoni,
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
säikkyen suurta joukkoa ja kaiken heimon ylenkatsetta peljäten, niin että pysyin hiljaa, ovestani ulkonematta?
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
Oi, jospa joku kuuntelisi minua! Katso, tuossa on puumerkkini! Kaikkivaltias vastatkoon minulle! Jospa saisin riitapuoleni kirjoittamaan syytekirjan!
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
Totisesti, olkapäälläni sitä kantaisin, sitoisin sen päähäni seppeleeksi.
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
Tekisin hänelle tilin kaikista askeleistani ja astuisin hänen eteensä niinkuin ruhtinas.
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
Jos peltoni huusi minua vastaan ja sen vaot kaikki itkivät,
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
jos kulutin sen voiman maksamatta ja saatoin sen haltijat huokaamaan,
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
niin kasvakoon nisun sijasta orjantappuroita ja ohran sijasta rikkaruohoa." Tähän päättyvät Jobin puheet.