< Ayuba 31 >

1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
“I made a covenant with my eyes; how then should I look lustfully at a young woman?
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
For what is the portion from God above, and the heritage from the Almighty on high?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
Is it not calamity to the unrighteous, and disaster to the workers of iniquity?
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
Doesn’t he see my ways, and count all my steps?
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
“If I have walked with falsehood, and my foot has hurried to deceit
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
(let me be weighed in an even balance, that God may know my integrity);
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
if my step has turned out of the way, if my heart walked after my eyes, if any defilement has stuck to my hands,
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
then let me sow, and let another eat. Yes, let the produce of my field be rooted out.
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
“If my heart has been enticed to a woman, and I have laid wait at my neighbor’s door,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
then let my wife grind for another, and let others sleep with her.
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
For that would be a heinous crime. Yes, it would be an iniquity to be punished by the judges,
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
for it is a fire that consumes to destruction, and would root out all my increase.
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
“If I have despised the cause of my male servant or of my female servant, when they contended with me,
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
what then will I do when God rises up? When he visits, what will I answer him?
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
Didn’t he who made me in the womb make him? Didn’t one fashion us in the womb?
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
“If I have withheld the poor from their desire, or have caused the eyes of the widow to fail,
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
or have eaten my morsel alone, and the fatherless has not eaten of it
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
(no, from my youth he grew up with me as with a father, I have guided her from my mother’s womb);
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
if I have seen any perish for want of clothing, or that the needy had no covering;
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
if his heart hasn’t blessed me, if he hasn’t been warmed with my sheep’s fleece;
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
if I have lifted up my hand against the fatherless, because I saw my help in the gate;
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
then let my shoulder fall from the shoulder blade, and my arm be broken from the bone.
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
For calamity from God is a terror to me. Because of his majesty, I can do nothing.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
“If I have made gold my hope, and have said to the fine gold, ‘You are my confidence;’
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
If I have rejoiced because my wealth was great, and because my hand had gotten much;
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
if I have seen the sun when it shined, or the moon moving in splendor,
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
and my heart has been secretly enticed, and my hand threw a kiss from my mouth;
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
this also would be an iniquity to be punished by the judges, for I would have denied the God who is above.
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
“If I have rejoiced at the destruction of him who hated me, or lifted up myself when evil found him
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
(I have certainly not allowed my mouth to sin by asking his life with a curse);
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
if the men of my tent have not said, ‘Who can find one who has not been filled with his meat?’
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
(the foreigner has not camped in the street, but I have opened my doors to the traveler);
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
if like Adam I have covered my transgressions, by hiding my iniquity in my heart,
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
because I feared the great multitude, and the contempt of families terrified me, so that I kept silence, and didn’t go out of the door—
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
oh that I had one to hear me! Behold, here is my signature! Let the Almighty answer me! Let the accuser write my indictment!
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
Surely I would carry it on my shoulder, and I would bind it to me as a crown.
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
I would declare to him the number of my steps. I would go near to him like a prince.
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
If my land cries out against me, and its furrows weep together;
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
if I have eaten its fruits without money, or have caused its owners to lose their life,
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
let briers grow instead of wheat, and stinkweed instead of barley.” The words of Job are ended.

< Ayuba 31 >