< Ayuba 31 >
1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
A covenant, I solemnised for mine eyes, —How then could I gaze upon a virgin?
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
Or what would have been my portion of GOD from above? Or what inheritance of the Almighty from on high?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
Is there not calamity, for the perverse? and misfortune, for the workers of iniquity?
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
Would, he, not see my ways? and of all my steps, take account?
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
Verily I walked not in falsity, nor did my foot haste unto deceit: —
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
Let him weigh me in balances of righteousness, —and let GOD take note of mine integrity!
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
If my goings have swerved from the way, —and, after mine eyes, hath gone my heart, and, to my hands, hath adhered any stain,
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
Let me sow but, another, eat. And let, what I have springing up, be uprooted!
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
If my heart hath been enticed unto a woman, or, by the door of my neighbour, I have lien in wait,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
Let my wife, grind to another, and, over her, let others bend!
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
Surely that had been a shameful thing! and that an iniquity for the judges!
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
Surely, a fire, had that been, which, unto destruction, would have consumed, and, of all mine increase, had it torn up the root.
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
If I refused the right of my servant, or my handmaid, when they contended with me,
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
What then could I have done when GOD rose up? And, when he visited, what could I have answered him?
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
Did not he who, in the womb, made me, make him? And is not he who formed us in the body one?
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
If I withheld—from pleasure—the poor, or, the eyes of the widow, I dimmed;
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
Or, used to eat my morsel alone, so that the fatherless did not eat thereof;
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
Surely, from my youth, he grew up to me, as to a father, and, from my birth, I acted as guide to her:
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
If I saw one perishing for lack of clothing, or that the needy had no covering;
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
If his loins did not bless me, or if, with the fleece of my lambs, he did not warm himself;
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
If I shook—against the fatherless—my hand, when I saw, in the gate, his need of my help,
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
Let, my shoulder, from the shoulder-blade, fall, and, my arm, from the upper bone, be broken;
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
For, a dread unto me, was calamity from GOD, and, from his majesty, I could not escape.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
If I made gold my stay, and, to precious metal, said, My confidence!
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
If I rejoiced because great was my substance, and, an abundance, my hand had discovered;
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
If I looked at the sun, when it flashed forth light, or at the moon, majestically marching along;
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
And befooled secretly was my heart, so that my hand kissed my mouth,
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
That too, had been a judicial iniquity, For I should have been false to GOD, above.
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
If rejoiced in the misfortune of him that hated me, or exulted when calamity found him; —
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
Neither did I suffer my palate to sin, by asking, with a curse, for his life:
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
If the men of my household have not said, Oh for some of his flesh—we cannot get filled,
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
Outside, the sojourner lodged not for the night, My doors—to the wayfarer, I threw open.
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
If I covered, like Adam, my transgressions, by hiding in my bosom mine iniquity,
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
Then let me be made to tremble at a great throng, yea let, the contempt of families, terrify me, so that, keeping silence, I shall not go out of the door!
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
Oh that I had one to hear me, Lo! my crossmark, May, the Almighty, answer me! And would that, a book, mine opponent had written!
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
Oh! would I not, upon my shoulder, lift it, or bind it as a crown upon me;
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
The number of my footsteps, I would declare to him, Like a noble, would I draw near to him.
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
If, against me, my ground used to cry out, and, together, my ridges did weep;
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
If, the strength thereof, I used to eat, without payment, and, the soul of the holders thereof, I made groan;
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
Instead of wheat, let there come forth bramble, and, instead of barley, a bad-smelling weed! Ended are the words of Job.