< Ayuba 31 >

1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
“I have made a covenant with my eyes. How then could I gaze with desire at a virgin?
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
For what is the allotment of God from above, or the heritage from the Almighty on high?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
Does not disaster come to the unjust and calamity to the workers of iniquity?
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
Does He not see my ways and count my every step?
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
If I have walked in falsehood or my foot has rushed to deceit,
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
let God weigh me with honest scales, that He may know my integrity.
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
If my steps have turned from the path, if my heart has followed my eyes, or if impurity has stuck to my hands,
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
then may another eat what I have sown, and may my crops be uprooted.
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
If my heart has been enticed by my neighbor’s wife, or I have lurked at his door,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
then may my own wife grind grain for another, and may other men sleep with her.
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
For that would be a heinous crime, an iniquity to be judged.
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
For it is a fire that burns down to Abaddon; it would root out my entire harvest.
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
If I have rejected the cause of my manservant or maidservant when they made a complaint against me,
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
what will I do when God rises to judge? How will I answer when called to account?
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
Did not He who made me in the womb also make them? Did not the same One form us in the womb?
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
If I have denied the desires of the poor or allowed the widow’s eyes to fail,
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
if I have eaten my morsel alone, not sharing it with the fatherless—
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
though from my youth I reared him as would a father, and from my mother’s womb I guided the widow—
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
if I have seen one perish for lack of clothing, or a needy man without a cloak,
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
if his heart has not blessed me for warming him with the fleece of my sheep,
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
if I have lifted up my hand against the fatherless because I saw that I had support in the gate,
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
then may my arm fall from my shoulder and be torn from its socket.
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
For calamity from God terrifies me, and His splendor I cannot overpower.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
If I have put my trust in gold or called pure gold my security,
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
if I have rejoiced in my great wealth because my hand had gained so much,
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
if I have beheld the sun in its radiance or the moon moving in splendor,
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
so that my heart was secretly enticed and my hand threw a kiss from my mouth,
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
this would also be an iniquity to be judged, for I would have denied God on high.
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
If I have rejoiced in my enemy’s ruin, or exulted when evil befell him—
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
I have not allowed my mouth to sin by asking for his life with a curse—
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
if the men of my house have not said, ‘Who is there who has not had his fill?’—
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
but no stranger had to lodge on the street, for my door has been open to the traveler—
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
if I have covered my transgressions like Adam by hiding my guilt in my heart,
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
because I greatly feared the crowds and the contempt of the clans terrified me, so that I kept silent and would not go outside—
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
(Oh, that I had one to hear me! Here is my signature. Let the Almighty answer me; let my accuser compose an indictment.
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
Surely I would carry it on my shoulder and wear it like a crown.
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
I would give account of all my steps; I would approach Him like a prince.)—
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
if my land cries out against me and its furrows weep together,
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
if I have devoured its produce without payment or broken the spirit of its tenants,
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
then let briers grow instead of wheat and stinkweed instead of barley.” Thus conclude the words of Job.

< Ayuba 31 >