< Ayuba 31 >

1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
我同我的眼立了約,決不注視處女。
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
天主由上所注定的一分是什麼﹖全能者由高處所給的產業是什麼﹖
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
豈不是為惡人注定了喪亡,為作孽的人注定了災殃﹖
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
他豈不監視我的行徑,計算我的腳步﹖
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
我若與虛偽同行,我的腳若趨向詭詐,
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
願天主以公正的天平秤量我,他必知道我的純正。
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
我的腳步如果離開了正道,我的心如果隨從了眼目之所見,我的手若持有不潔,
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
那麼,我種的,情願讓別人來吃;我栽的,情願讓別人拔出。
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
我的心如果為婦女所迷,我如果曾在鄰人門口等候婦女,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
就讓我的妻子給人推磨,讓別人與她同寢。
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
因為這是淫行,是應受嚴刑的罪惡;
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
是一種焚燒至毀滅的火,燒盡我全部產業的火。
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
當我的僕婢與我爭執時,我若輕視他們的權利,
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
天主起來時,我可怎麼辦呢﹖他若追問,我可怎樣回答﹖
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
在母胎造成我的,不是也造了他們﹖在母胎形成我們的,不是只有他一個﹖
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
我何時曾拒絕了窮苦人的渴望,我何時曾使寡婦的眼目頹喪﹖
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
我何時獨自吃食物,而沒有與孤兒共享﹖
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
因為天主自我幼年,就像父親教養了我;自我出了母胎,就引導了我。
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
如果我見了無衣蔽體的乞丐,無遮蓋的窮人,
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
如果他的心沒有向我道謝,沒有以我的羊毛獲得溫暖,
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
如果我在城門口見有支持我者,就舉手攻擊無罪者,
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
那麼,讓我的肩由胛骨脫落,我的胳膊由肘處折斷!
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
因為天主的懲罰使我驚駭,因他的威嚴,我站立不住。
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
我何嘗以黃金為依靠,對純金說過:「你是我的靠山﹖」
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
我何嘗因財產豐富,手賺的多而喜樂過﹖
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
我何時見太陽照耀,月亮皎潔徐行,
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
我的心遂暗中受到迷惑,我的口遂親手送吻﹖
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
這也是應受嚴罰的罪過,因為我背棄了至高的天主。
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
我何時慶幸恨我者遭殃,見他遭遇不幸而得意﹖
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
其實,我沒有容我的口犯罪,詛咒過他的性命。
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
我帳幕內的人是否有人說過:「某人沒有吃飽主人給的肉﹖」
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
外方人沒有睡在露天地裏,我的門常為旅客敞開。
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
我豈像凡人一樣,掩飾過我的過犯,把邪惡隱藏在胸中﹖
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
我豈怕群眾的吵鬧﹖親族的謾罵豈能嚇住我,使我不敢作聲,杜門不出﹖
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
惟願天主俯聽我,這是我最後的要求:願全能者答覆我! 我的對方所寫的狀詞,
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
我要把它背在我肩上,編成我的冠冕。
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
我將像王侯一樣走向他面前,向他一一陳述我的行為。--約伯的話至此為止。
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
我的田地若控告我,犁溝若一同哀訴,
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
我若吃田中的產物而不付代價,或叫地主心靈悲傷,
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
願此地不再長小麥而長荊棘,不長大麥而長惡草。

< Ayuba 31 >