< Ayuba 30 >
1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
MAS ahora los más mozos de días que yo, se ríen de mí; cuyos padres yo desdeñara ponerlos con los perros de mi ganado.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
Porque ¿para qué yo habría menester la fuerza de sus manos, en los cuales había perecido con el tiempo?
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
Por causa de la pobreza y del hambre [andaban] solos; huían á la soledad, á lugar tenebroso, asolado y desierto.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
Que cogían malvas entre los arbustos, y raíces de enebro para calentarse.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
Eran echados de entre [las gentes], y todos les daban grita como al ladrón.
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
Habitaban en las barrancas de los arroyos, en las cavernas de la tierra, y en las rocas.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
Bramaban entre las matas, y se reunían debajo de las espinas.
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
Hijos de viles, y hombres sin nombre, más bajos que la misma tierra.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Y ahora yo soy su canción, y he sido hecho su refrán.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Abomínanme, aléjanse de mí, y aun de mi rostro no detuvieron su saliva.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Porque [Dios] desató mi cuerda, y me afligió, por eso se desenfrenaron delante de mi rostro.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
A la mano derecha se levantaron los jóvenes; empujaron mis pies, y sentaron contra mí las vías de su ruina.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Mi senda desbarataron, aprovecháronse de mi quebrantamiento, contra los cuales no hubo ayudador.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Vinieron como por portillo ancho, revolviéronse á [mi] calamidad.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Hanse revuelto turbaciones sobre mí; combatieron como viento mi alma, y mi salud pasó como nube.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
Y ahora mi alma está derramada en mí; días de aflicción me han aprehendido.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
De noche taladra sobre mí mis huesos, y mis pulsos no reposan.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Con la grande copia [de materia] mi vestidura está demudada; cíñeme como el cuello de mi túnica.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Derribóme en el lodo, y soy semejante al polvo y á la ceniza.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Clamo á ti, y no me oyes; preséntome, y no me atiendes.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Haste tornado cruel para mí: con la fortaleza de tu mano me amenazas.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Levantásteme, é hicísteme cabalgar sobre el viento, y disolviste mi sustancia.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Porque yo conozco que me reduces á la muerte; y á la casa determinada á todo viviente.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Mas él no extenderá la mano contra el sepulcro; ¿clamarán [los sepultados] cuando él los quebrantare?
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
¿No lloré yo al afligido? Y mi alma ¿no se entristeció sobre el menesteroso?
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
Cuando esperaba yo el bien, entonces vino el mal; y cuando esperaba luz, la oscuridad vino.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
Mis entrañas hierven, y no reposan; días de aflicción me han sobrecogido.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Denegrido ando, y no por el sol: levantádome he en la congregación, y clamado.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
He venido á ser hermano de los dragones, y compañero de los buhos.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Mi piel está denegrida sobre mí, y mis huesos se secaron con ardentía.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
Y hase tornado mi arpa en luto, y mi órgano en voz de lamentadores.