< Ayuba 30 >

1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
“Pero ahora los que son más jóvenes que yo se burlan de mí, cuyos padres consideré indignos de poner con mis perros pastores.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
¿De qué me sirve la fuerza de sus manos? hombres en los que la edad madura ha perecido?
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
Están demacrados por la carencia y el hambre. Roen la tierra seca, en la penumbra del desperdicio y la desolación.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
Arrancan hierbas saladas junto a los arbustos. Las raíces del árbol de la retama son su alimento.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
Son expulsados de entre los hombres. Lloran tras ellos como tras un ladrón,
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
para que vivan en valles espantosos, y en agujeros de la tierra y de las rocas.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
Rebuznan entre los arbustos. Están reunidos bajo las ortigas.
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
Son hijos de locos, sí, hijos de malvados. Fueron expulsados a latigazos de la tierra.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
“Ahora me he convertido en su canción. Sí, soy un sinónimo para ellos.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Me aborrecen, se alejan de mí, y no duden en escupirme a la cara.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Porque ha desatado su cuerda y me ha afligido; y se han desprendido de la restricción ante mí.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
A mi derecha se levanta la chusma. Me apartan los pies. Ellos lanzan sus caminos de destrucción contra mí.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Marcan mi camino. Promueven mi destrucción sin la ayuda de nadie.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Como a través de una amplia brecha llegan. Se enrollan en medio de la ruina.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Los terrores se han vuelto contra mí. Persiguen mi honor como el viento. Mi bienestar ha pasado como una nube.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
“Ahora mi alma se derrama dentro de mí. Los días de aflicción se han apoderado de mí.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
En la estación nocturna mis huesos están calados en mí, y los dolores que me roen no tienen descanso.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Mi vestimenta está desfigurada por una gran fuerza. Me ata como el cuello de mi túnica.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Me ha arrojado al fango. Me he convertido en polvo y cenizas.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Clamo a ti, y no me respondes. Me pongo de pie, y tú me miras.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Te has vuelto cruel conmigo. Con la fuerza de tu mano me persigues.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Me alzas al viento y me conduces con él. Me disuelves en la tormenta.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Porque sé que me llevarás a la muerte, a la casa designada para toda la vida.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
“Sin embargo, ¿no se tiende la mano en su caída? ¿O en su calamidad, por tanto, clamar por ayuda?
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
¿No lloré por el que estaba en apuros? ¿No se afligió mi alma por los necesitados?
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
Cuando buscaba el bien, vino el mal. Cuando esperaba la luz, llegó la oscuridad.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
Mi corazón está turbado y no descansa. Me han llegado días de aflicción.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Voy de luto sin el sol. Me pongo de pie en la asamblea y pido ayuda.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
Soy hermano de los chacales, y compañera de los avestruces.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Mi piel se ennegrece y se desprende de mí. Mis huesos están quemados por el calor.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
Por eso mi arpa se ha convertido en luto, y mi pipa en la voz de los que lloran.

< Ayuba 30 >