< Ayuba 30 >

1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
Pero ahora se ríen de mí personas mucho más jóvenes que yo; personas a cuyos padres no pondría a trabajar con mis perros pastores.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
Son demasiado débiles para serme útiles y están agotados.
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
Adelgazados por el hambre y la necesidad, tratan de comer la tierra seca en el desierto oscuro y desolado.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
Allí recogen hierbas del desierto y las hojas de los arbustos, y comen las raíces de las retamas.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
Fueron expulsados de la comunidad.
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
La gente gritaba tras ellos como si fueran ladrones. Tienen que vivir en barrancos peligrosos, en cuevas y entre las rocas.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
Gritan como animales entre los arbustos; se acurrucan entre la maleza para refugiarse.
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
Son gente insensata, sin nombre, que ha sido expulsada de la tierra.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Pero ahora se burlan de mí en sus cantos; ¡me he convertido en un chiste para ellos!
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Me desprecian y rehúyen; no dudan en escupirme a la cara.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Dios ha aflojado la cuerda de mi arco y me ha humillado.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
La chusma se levanta contra mí, y me hace correr; como una ciudad sitiada planifican formas de destruirme.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Cortan mi vía de escape; provocan mi caída y lo hacen sin ayuda de nadie.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Entran por una amplia brecha; se precipitan mientras el muro se derrumba.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Me invaden los terrores; mi honor se lo lleva el viento; mi salvación se desvanece como una nube.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
Y ahora mi vida se desvanece; cada día la desesperación me atenaza.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
Por la noche mis huesos agonizan; el dolor me roe y no cesa.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Dios me agarra bruscamente por la ropa; me tira del cuello de la camisa.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Me ha arrojado al barro; me ha humillado como polvo y ceniza.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Dios, clamo a ti, pero no respondes; me presento ante ti, pero ni siquiera te fijas en mí.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Te has vuelto cruel conmigo; usas tu poder para hacerme sufrir.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Me levantas y me llevas en el viento; me arrojas en el torbellino.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Sé que me llevas a la muerte, al lugar donde van todos los vivos.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
¿Quién querría dar una patada a un hombre cuando está abatido, cuando claman por ayuda en su momento de dificultad?
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
¿No lloré por los que pasaban por momentos difíciles? ¿No me afligí por lo que sufrían los pobres?
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
Pero cuando busqué el bien, sólo vino el mal, y cuando esperé la luz, todo lo que vino fue oscuridad.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
En mi interior hay confusión, nunca se detiene; me enfrento a días de desesperación.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Estoy tan deprimido; ver el sol no ayuda. Me pongo de pie en la asamblea y clamo por ayuda.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
Soy como un hermano de los chacales, un compañero de los búhos.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Mi piel se ennegrece sobre mí; y mis huesos arden dentro de mí.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
Mi lira sólo toca canciones tristes, y mi pipa es la voz de los que lloran.

< Ayuba 30 >