< Ayuba 30 >
1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
Porém agora riem de mim os mais jovens do que eu, cujos pais eu havia desdenhado até de os pôr com os cães de meu rebanho.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
De que também me serviria força de suas mãos, nos quais o vigor já pereceu?
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
Por causa da pobreza e da fome andavam sós; roem na terra seca, no lugar desolado e deserto em trevas.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
Que colhiam malvas entre os arbustos, e seu alimento eram as raízes dos zimbros.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
Do meio [das pessoas] eram expulsos, e gritavam contra eles, como a um ladrão.
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
Habitavam nos barrancos dos ribeiros secos, nos buracos da terra, e nas rochas.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
Bramavam entre os arbustos, e se ajuntavam debaixo das urtigas.
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
Eram filhos de tolos, filhos sem nome, e expulsos de [sua] terra.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Porém agora sirvo-lhes de chacota, e sou para eles um provérbio de escárnio.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Eles me abominam [e] se afastam de mim; porém não hesitam em cuspir no meu rosto.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Pois [Deus] desatou minha corda, e me oprimiu; por isso tiraram [de si] todo constrangimento perante meu rosto.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
À direita os jovens se levantam; empurram meus pés, e preparam contra mim seus caminhos de destruição.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Destroem meu caminho, e promovem minha miséria, sem necessitarem que alguém os ajude.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Eles vêm [contra mim] como que por uma brecha larga, [e] revolvem-se entre a desolação.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Pavores se voltam contra mim; perseguem minha honra como o vento, e como nuvem passou minha prosperidade.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
Por isso agora minha alma se derrama em mim; dias de aflição têm me tomado.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
De noite meus ossos se furam em mim, e meus pulsos não descansam.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Por grande força [de Deus] minha roupa está estragada; ele me prendeu como a gola de minha roupa.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Lançou-me na lama, e fiquei semelhante ao pó e à cinza.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Clamo a ti, porém tu não me respondes; eu fico de pé, porém tu ficas [apenas] olhando para mim.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Tu te tornaste cruel para comigo; com a força de tua mão tu me atacas.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Levantas-me sobre o vento, [e] me fazes cavalgar [sobre ele]; e dissolves o meu ser.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Porque eu sei que me levarás à morte; e à casa determinada a todos os viventes.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Porém não se estende a mão para quem está em ruínas, quando clamam em sua opressão?
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
Por acaso eu não chorei pelo que estava em dificuldade, [e] minha alma não se angustiou pelo necessitado?
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
Quando eu esperava o bem, então veio o mal; quando eu esperava a luz, veio a escuridão.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
Minhas entranhas fervem, e não se aquietam; dias de aflição me confrontam.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Ando escurecido, mas não pelo sol; levanto-me na congregação, e clamo por socorro.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
Tornei-me irmão dos chacais, e companheiro dos avestruzes.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Minha pele se escureceu sobre mim, e meus ossos se inflamam de febre.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
Por isso minha harpa passou a ser para lamentação, e minha flauta para vozes dos que choram.