< Ayuba 30 >
1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
Porém agora se riem de mim os de menos edade do que eu, cujos paes eu teria desdenhado de pôr com os cães do meu rebanho.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
De que tambem me serviria a força das suas mãos? já de velhice se tinham esgotado n'elles.
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
De mingua e fome andavam sós, e recolhiam-se para os logares seccos, tenebrosos, assolados e desertos.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
Apanhavam malvas junto aos arbustos, e o seu mantimento eram as raizes dos zimbros.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
Do meio dos homens foram expulsos, e gritavam contra elles, como contra o ladrão:
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
Para habitarem nos barrancos dos valles, e nas cavernas da terra e das rochas.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
Bramavam entre os arbustos, e ajuntavam-se debaixo das ortigas.
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
Eram filhos de doidos, e filhos de gente sem nome, e da terra foram expulsos.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Porém agora sou a sua canção, e lhes sirvo de rifão.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Abominam-me, e fogem para longe de mim, e do meu rosto não reteem o seu escarro.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Porque Deus desatou o meu cordão, e me opprimiu, pelo que sacudiram de si o freio perante o meu rosto.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
Á direita se levantam os moços; empurram os meus pés, e preparam contra mim os seus caminhos de destruição.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Desbarataram-me o meu caminho: promovem a minha miseria: não teem ajudador.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Veem contra mim como por uma grande brecha, e revolvem-se entre a assolação.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Sobrevieram-me pavores; como vento perseguem a minha honra, e como nuvem passou a minha felicidade.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
E agora derrama-se em mim a minha alma: os dias da afflicção se apoderaram de mim.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
De noite se me traspassam os meus ossos, e os pulsos das minhas veias não descançam.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Pela grandeza da força das dôres se demudou o meu vestido, e elle como o cabeção da minha tunica me cinge.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Lançou-me na lama, e fiquei similhante ao pó e á cinza.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Clamo a ti, porém tu não me respondes: estou em pé, porém para mim não attentas.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Tornaste-te a ser cruel contra mim: com a força da tua mão resistes violentamente.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Levantas-me sobre o vento, fazes-me cavalgar sobre elle, e derretes-me o ser.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Porque eu sei que me levarás á morte e á casa do ajuntamento determinado a todos os viventes.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Porém não estenderá a mão para o montão de terra, se houve clamor n'elles contra mim na sua desventura.
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
Porventura, não chorei sobre aquelle que estava afflicto? ou não se angustiou a minha alma pelo necessitado?
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
Todavia aguardando eu o bem, então me veiu o mal, e esperando eu a luz, veiu a escuridão.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
As minhas entranhas ferveram e não estão quietas: os dias da afflicção me surprehenderam.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Denegrido ando, porém não do sol, e, levantando-me na congregação, clamo por soccorro.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
Irmão me fiz dos dragões, e companheiro dos abestruzes.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Ennegreceu-se a minha pelle sobre mim, e os meus ossos estão queimados do calor.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
Pelo que se trocou a minha harmonia em lamentação, e o meu orgão em voz dos que choram.