< Ayuba 30 >
1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
nunc autem derident me iuniores tempore quorum non dignabar patres ponere cum canibus gregis mei
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
quorum virtus manuum erat mihi pro nihilo et vita ipsa putabantur indigni
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
egestate et fame steriles qui rodebant in solitudine squalentes calamitate et miseria
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
et mandebant herbas et arborum cortices et radix iuniperorum erat cibus eorum
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
qui de convallibus ista rapientes cum singula repperissent ad ea cum clamore currebant
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
in desertis habitabant torrentium et in cavernis terrae vel super glaream
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
qui inter huiuscemodi laetabantur et esse sub sentibus delicias conputabant
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
filii stultorum et ignobilium et in terra penitus non parentes
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
nunc in eorum canticum versus sum et factus sum eis proverbium
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
abominantur me et longe fugiunt a me et faciem meam conspuere non verentur
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
faretram enim suam aperuit et adflixit me et frenum posuit in os meum
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
ad dexteram orientis calamitatis meae ilico surrexerunt pedes meos subverterunt et oppresserunt quasi fluctibus semitis suis
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
dissipaverunt itinera mea insidiati sunt mihi et praevaluerunt et non fuit qui ferret auxilium
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
quasi rupto muro et aperta ianua inruerunt super me et ad meas miserias devoluti sunt
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
redactus sum in nihili abstulisti quasi ventus desiderium meum et velut nubes pertransiit salus mea
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
nunc autem in memet ipso marcescit anima mea et possident me dies adflictionis
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
nocte os meum perforatur doloribus et qui me comedunt non dormiunt
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
in multitudine eorum consumitur vestimentum meum et quasi capitio tunicae sic cinxerunt me
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
conparatus sum luto et adsimilatus favillae et cineri
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
clamo ad te et non exaudis me sto et non respicis me
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
mutatus es mihi in crudelem et in duritia manus tuae adversaris mihi
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
elevasti me et quasi super ventum ponens elisisti me valide
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
scio quia morti tradas me ubi constituta domus est omni viventi
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
verumtamen non ad consumptionem eorum emittis manum tuam et si corruerint ipse salvabis
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
flebam quondam super eum qui adflictus erat et conpatiebatur anima mea pauperi
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
expectabam bona et venerunt mihi mala praestolabar lucem et eruperunt tenebrae
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
interiora mea efferbuerunt absque ulla requie praevenerunt me dies adflictionis
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
maerens incedebam sine furore consurgens in turba clamavi
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
frater fui draconum et socius strutionum
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
cutis mea denigrata est super me et ossa mea aruerunt prae caumate
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
versa est in luctum cithara mea et organum meum in vocem flentium