< Ayuba 30 >
1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
Nunc autem derident me juniores tempore, quorum non dignabar patres ponere cum canibus gregis mei:
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
quorum virtus manuum mihi erat pro nihilo, et vita ipsa putabantur indigni:
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
egestate et fame steriles, qui rodebant in solitudine, squallentes calamitate et miseria.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
Et mandebant herbas, et arborum cortices, et radix juniperorum erat cibus eorum:
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
qui de convallibus ista rapientes, cum singula reperissent, ad ea cum clamore currebant.
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
In desertis habitabant torrentium, et in cavernis terræ, vel super glaream:
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
qui inter hujuscemodi lætabantur, et esse sub sentibus delicias computabant:
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
filii stultorum et ignobilium, et in terra penitus non parentes.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Nunc in eorum canticum versus sum, et factus sum eis in proverbium.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Abominantur me, et longe fugiunt a me, et faciem meam conspuere non verentur.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Pharetram enim suam aperuit, et afflixit me, et frenum posuit in os meum.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
Ad dexteram orientis calamitates meæ illico surrexerunt: pedes meos subverterunt, et oppresserunt quasi fluctibus semitis suis.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Dissipaverunt itinera mea; insidiati sunt mihi, et prævaluerunt: et non fuit qui ferret auxilium.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Quasi rupto muro, et aperta janua, irruerunt super me, et ad meas miserias devoluti sunt.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Redactus sum in nihilum: abstulisti quasi ventus desiderium meum, et velut nubes pertransiit salus mea.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
Nunc autem in memetipso marcescit anima mea, et possident me dies afflictionis.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
Nocte os meum perforatur doloribus, et qui me comedunt, non dormiunt.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
In multitudine eorum consumitur vestimentum meum, et quasi capitio tunicæ succinxerunt me.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Comparatus sum luto, et assimilatus sum favillæ et cineri.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Clamo ad te, et non exaudis me: sto, et non respicis me.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Mutatus es mihi in crudelem, et in duritia manus tuæ adversaris mihi.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Elevasti me, et quasi super ventum ponens; elisisti me valide.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Scio quia morti trades me, ubi constituta est domus omni viventi.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Verumtamen non ad consumptionem eorum emittis manum tuam: et si corruerint, ipse salvabis.
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
Flebam quondam super eo qui afflictus erat, et compatiebatur anima mea pauperi.
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
Expectabam bona, et venerunt mihi mala: præstolabar lucem, et eruperunt tenebræ.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
Interiora mea efferbuerunt absque ulla requie: prævenerunt me dies afflictionis.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Mœrens incedebam sine furore; consurgens, in turba clamabam.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
Frater fui draconum, et socius struthionum.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Cutis mea denigrata est super me, et ossa mea aruerunt præ caumate.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
Versa est in luctum cithara mea, et organum meum in vocem flentium.