< Ayuba 30 >

1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
Nun aber lachen mein, die jünger sind denn ich, welcher Väter ich verachtet hätte, zu stellen unter meine Schafhunde,
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
welcher Vermögen ich für nichts hielt, die nicht zum Alter kommen konnten,
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
die vor Hunger und Kummer einsam flohen in die Einöde, neulich verdorben und elend worden,
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
die da Nesseln ausrauften um die Büsche, und Wacholderwurzel war ihre Speise;
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
und wenn sie die herausrissen, jauchzeten sie drüber wie ein Dieb.
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
An den grausamen Bächen wohneten sie, in den Löchern der Erde und Steinritzen.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
Zwischen den Büschen riefen sie und unter den Disteln sammelten sie,
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
die Kinder loser und verachteter Leute, die die Geringsten im Lande waren.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Nun bin ich ihr Saitenspiel worden und muß ihr Märlein sein.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Sie haben einen Greuel an mir und machen sich ferne von mir und schonen nicht, vor meinem Angesicht zu speien.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Sie haben mein Seil ausgespannet und mich zunichte gemacht und das Meine abgezäumet.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
Zur Rechten, da ich grünete, haben sie sich wieder mich gesetzt und haben meinen Fuß ausgestoßen; und haben über mich einen Weg gemacht, mich zu verderben.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Sie haben meine Steige zerbrochen; es war ihnen so leicht, mich zu beschädigen, daß sie keiner Hilfe dazu bedurften.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Sie sind kommen, wie zur weiten Lücke herein, und sind ohne Ordnung dahergefallen.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Schrecken hat sich gegen mich gekehret und hat verfolget wie der Wind meine HERRLIchkeit und wie eine laufende Wolke meinen glückseligen Stand.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
Nun aber gießt sich aus meine Seele über mich, und mich hat ergriffen die elende Zeit.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
Des Nachts wird mein Gebein durchbohret allenthalben, und die mich jagen, legen sich nicht schlafen.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Durch die Menge der Kraft werde ich anders und anders gekleidet; und man gürtet mich damit wie mit dem Loch meines Rocks.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Man hat mich in Kot getreten und gleich geachtet dem Staub und Asche.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Schreie ich zu dir, so antwortest du mir nicht; trete ich hervor, so achtest du nicht auf mich.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Du bist mir verwandelt in einen Grausamen und zeigest deinen Gram an mir mit der Stärke deiner Hand.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Du hebest mich auf und lässest mich auf dem Winde fahren und zerschmelzest mich kräftiglich.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Denn ich weiß, du wirst mich dem Tode überantworten; da ist das bestimmte Haus aller Lebendigen.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Doch wird er nicht die Hand ausstrecken ins Beinhaus, und werden nicht schreien vor seinem Verderben.
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
Ich weinete ja in der harten Zeit, und meine Seele jammerte der Armen.
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
Ich wartete des Guten, und kommt das Böse; ich hoffte aufs Licht, und kommt Finsternis.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
Meine Eingeweide sieden und hören nicht auf; mich hat überfallen die elende Zeit.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Ich gehe schwarz einher, und brennet mich doch keine Sonne nicht; ich stehe auf in der Gemeine und schreie.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
Ich bin ein Bruder der Schlangen und ein Geselle der Straußen.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Meine Haut über mir ist schwarz worden, und meine Gebeine sind verdorret vor Hitze.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
Meine Harfe ist eine Klage worden und meine Pfeife ein Weinen.

< Ayuba 30 >