< Ayuba 30 >

1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
Mais, maintenant, des hommes plus jeunes que moi se moquent de moi, des hommes dont je n'aurais pas daigné mettre les pères avec les chiens de mon troupeau.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
Et qu'aurais-je pu faire de la force de leurs mains? En eux avait péri toute vigueur.
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
Exténués par la disette et la faim, ils broutent les lieux arides, depuis longtemps désolés et déserts.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
Ils cueillent l'herbe sauvage près des buissons, et la racine des genêts est leur nourriture.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
On les chasse du milieu des hommes; on crie après eux comme après un larron;
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
Ils habitent dans des torrents affreux, dans les trous de la terre, et parmi les rochers.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
On les entend braire dans les buissons, ils s'étendent pêle-mêle sous les chardons;
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
Race impie, race sans nom, qui avait été chassée du pays!
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Et maintenant je suis le sujet de leurs chansons, et je fais la matière de leurs propos.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Ils m'ont en horreur, ils s'éloignent de moi; ils ne craignent pas de me cracher au visage.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Parce que Dieu a détendu la corde de mon arc et m'a humilié, ils ont secoué tout frein devant moi.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
Cette engeance se lève à ma droite; ils poussent mes pieds; ils construisent contre moi des routes pour me nuire;
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Ils rompent mon chemin, ils aident à ma ruine, eux à qui personne ne porterait secours.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Ils arrivent comme par une large brèche, ils se précipitent au milieu du fracas.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Toutes les terreurs se tournent contre moi, elles poursuivent ma prospérité comme le vent, et mon bonheur a passé comme un nuage!
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
Et maintenant mon âme se fond en moi, les jours d'affliction m'ont atteint;
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
La nuit perce mes os et les détache, et ceux qui me rongent ne dorment pas.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Par la violence extrême de mon mal, mon vêtement se déforme; il me serre comme le col de ma tunique.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Dieu m'a jeté dans la boue, et je ressemble à la poussière et à la cendre.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Je crie vers toi, et tu ne me réponds pas; je me tiens debout devant toi, et tu me considères!
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Tu es devenu cruel pour moi; tu t'opposes à moi avec toute la force de ton bras.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Tu m'enlèves, tu me fais chevaucher sur le vent, et tu me fais fondre au bruit de la tempête.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Oui, je sais bien que tu m'amènes à la mort, et dans la demeure, rendez-vous de tous les vivants.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Seulement, n'étendrait-on pas la main au milieu de la ruine? Et, dans sa calamité, ne serait-il donc pas permis de pousser un cri?
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
Ne pleurais-je pas sur l'homme qui passait de mauvais jours? Mon âme n'était-elle pas affligée à cause du pauvre
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
J'ai attendu le bonheur, et le malheur est arrivé. J'espérais la lumière, et les ténèbres sont venues.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
Mes entrailles bouillonnent sans repos; les jours d'affliction m'ont assailli.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Je marche tout noirci, et non par le soleil. Je me lève dans l'assemblée, et je crie.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
Je suis devenu le frère des chacals, et le compagnon des autruches.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Ma peau se noircit et tombe. Mes os sont brûlés par la fièvre.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
Ma harpe s'est changée en deuil, et mon luth en voix de pleurs.

< Ayuba 30 >