< Ayuba 30 >

1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
Mais maintenant ceux qui sont plus jeunes que moi, se moquent de moi; [ceux-là même] dont je n'aurais pas daigné mettre les pères avec les chiens de mon troupeau.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
Et en effet, de quoi m'eût servi la force de leurs mains? la vieillesse était périe en eux.
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
De disette et de faim ils se tenaient à l'écart, fuyant dans les lieux arides, ténébreux, désolés, et déserts.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
Ils coupaient des herbes sauvages auprès des arbrisseaux, et la racine des genévriers pour se chauffer.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
Ils étaient chassés d'entre les hommes, et on criait après eux comme après un larron.
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
Ils habitaient dans les creux des torrents, dans les trous de la terre et des rochers.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
Ils faisaient du bruit entre les arbrisseaux, et ils s'attroupaient entre les chardons.
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
Ce sont des hommes de néant, et sans nom, qui ont été abaissés plus bas que la terre.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Et maintenant je suis le sujet de leur chanson, et la matière de leur entretien.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Ils m'ont en abomination; ils se tiennent loin de moi; et ils ne craignent pas de me cracher au visage.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Parce que [Dieu] a détendu ma corde, et m'a affligé, ils ont secoué le frein devant moi.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
De jeunes gens, nouvellement nés, se placent à ma droite; ils poussent mes pieds, et je suis en butte à leur malice.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Ils ruinent mon sentier, ils augmentent mon affliction, sans qu'ils aient besoin que personne les aide.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Ils viennent [contre moi] comme par une brèche large, et ils se sont jetés [sur moi] à cause de ma désolation.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Les frayeurs se sont tournées vers moi, [et] comme un vent elles poursuivent mon âme; et ma délivrance s'est dissipée comme une nuée.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
C'est pourquoi maintenant mon âme se fond en moi; les jours d'affliction m'ont atteint.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
Il m'a percé de nuit les os, et mes artères n'ont point de relâche.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Il a changé mon vêtement par la grandeur de sa force, et il me serre de près, comme fait l'ouverture de ma tunique.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Il m'a jeté dans la boue, et je ressemble à la poussière et à la cendre.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Je crie à toi, et tu ne m'exauces point; je me tiens debout, et tu ne [me] regardes point.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Tu es pour moi sans compassion, tu me traites en ennemi par la force de ta main.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Tu m'as élevé [comme] sur le vent, et tu m'y as fait monter comme sur un chariot, et puis tu fais fondre toute ma substance.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Je sais donc que tu m'amèneras à la mort et dans la maison assignée à tous les vivants.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Mais il n'étendra pas sa main jusqu'au sépulcre. Quand il les aura tués, crieront-ils?
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
Ne pleurais-je pas pour l'amour de celui qui passait de mauvais jours; et mon âme n'était-elle pas affligée à cause du pauvre?
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
Cependant lorsque j'attendais le bien, le mal m'est arrivé; et quand j'espérais la clarté, les ténèbres sont venues.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
Mes entrailles sont dans une grande agitation, et ne peuvent se calmer; les jours d'affliction m'ont prévenu.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Je marche tout noirci, mais non pas du soleil; je me lève, je crie en pleine assemblée.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
Je suis devenu le frère des dragons, et le compagnon des hiboux.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Ma peau est devenue noire sur moi, et mes os sont desséchés par l'ardeur [qui me consume].
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
C'est pourquoi ma harpe s'est changée en lamentations, et mes orgues en des sons lugubres.

< Ayuba 30 >