< Ayuba 30 >

1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
Et maintenant j’excite les moqueries de gens plus jeunes que moi, dont les pères m’inspiraient trop de mépris pour les mettre avec les chiens de mon troupeau.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
Aussi bien, à quoi m’eût servi le concours de leurs mains? Pour eux il n’y a point de maturité.
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
Epuisés par les privations et la faim, ils rôdent dans le désert, lugubre région de désolation et d’horreur,
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
cueillant des plantes sauvages près des arbrisseaux, se nourrissant de la racine des genêts.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
On les chasse du milieu des hommes et on les poursuit de cris comme des voleurs.
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
Ils sont contraints d’habiter dans d’effrayants ravins, dans les excavations du sol et les crevasses des rochers.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
Ils grognent au milieu des buissons et s’entassent sous les broussailles;
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
troupe méprisable, gens sans aveu, ils se voient expulsés du pays!
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Et à présent, ils me chansonnent; je suis pour eux un thème à railleries.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Ils me témoignent leur dégoût, ils s’écartent de moi et ne se privent pas de me cracher à la figure.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
C’Est que Dieu a brisé les rênes que je tenais en mains, et il m’a humilié; ces gens ont secoué le frein que je leur imposais.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
A ma droite se lève une jeunesse insolente, qui fait glisser mes pas et se fraie vers moi ses routes de malheur.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Ils défoncent mon chemin, coopèrent à ma ruine, sans avoir besoin d’assistance.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Ils montent à' l’assaut comme par une large brèche, ils se précipitent au milieu du fracas.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Des terreurs me poursuivent, chassant comme le vent mon honneur; ma prospérité a passé comme un nuage.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
Et maintenant mon âme se fond en moi, les jours de misère m’ont enserré.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
La nuit ronge les os de mon corps, mes nerfs ne jouissent d’aucun repos.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Par l’extrême violence du choc mon vêtement se déforme: elle m’étreint comme l’encolure d’une tunique.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Dieu m’a plongé dans la fange, et j’ai l’air d’être poussière et cendre.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Je crie vers toi, et tu ne me réponds pas; je me tiens là, et tu me regardes fixement.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Tu es devenu inexorable pour moi, tu me combats avec toute la force de ta main.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Tu m’enlèves sur les ailes du vent, tu m’y fais chevaucher, et tu me fais fondre dans la tempête.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Car je sais bien que tu me mènes à la mort, au rendez-vous de tous les vivants.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Mais est-ce qu’on n’étend pas la main quand on s’effondre? Ne crie-t-on pas au secours lorsqu’on succombe au malheur?
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
Moi-même n’ai-je pas pleuré sur les victimes du sort? Mon cœur ne s’est-il point serré à la vue du malheureux?
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
J’Espérais le bien, et le mal a fondu sur moi; j’attendais la lumière, les ténèbres sont venues.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
Mes entrailles bouillonnent sans relâche, les jours de misère m’ont assailli.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Je marche tout noirci et non par le fait du soleil. Je me lève dans l’assemblée et pousse des cris.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
Je suis devenu le frère des chacals, le compagnon des autruches.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Ma peau, toute noircie, se détache de moi, et mes os sont brûlés par le feu de la fièvre.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
Et ainsi ma harpe s’est changée en instrument de deuil, et ma flûte émet des sanglots.

< Ayuba 30 >