< Ayuba 30 >

1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
But now they that are younger than I hold me in derision, Whose fathers I would have disdained to set with the dogs of my flock.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
Of what use to me would be even the strength of their hands, To whom old age is lost?
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
By want and hunger they are famished; They gnaw the dry desert, The darkness of desolate wastes.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
They gather purslain among the bushes, And the root of the broom is their bread.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
They are driven from the society of men; There is a cry after them as after a thief.
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
They dwell in gloomy valleys, In caves of the earth and in rocks.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
They bray among the bushes; Under the brambles are they stretched out.
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
An impious and low-born race, They are beaten out of the land.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
And now I am become their song; Yea, I am their by-word!
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
They abhor me, they stand aloof from me; They forbear not to spit before my face.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Yea, they let loose the reins, and humble me; They cast off the bridle before me.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
On my right hand riseth up the brood; They thrust away my feet; They cast up against me their destructive ways.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
They break up my path; They hasten my fall, —They who have no helper!
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
They come upon me as through a wide breach; Through the ruins they rush in upon me.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Terrors are turned against me; They pursue my prosperity like the wind, And my welfare passeth away like a cloud.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
And now my soul poureth itself out upon me; Days of affliction have taken hold of me.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
By night my bones are pierced; they are torn from me, And my gnawers take no rest.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Through the violence of my disease is my garment changed; It bindeth me about like the collar of my tunic.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
He hath cast me into the mire, And I am become like dust and ashes.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
I call upon Thee, but thou dost not hear me; I stand up before thee, but thou regardest me not.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Thou art become cruel to me; With thy strong hand dost thou lie in wait for me.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Thou liftest me up, and causest me to ride upon the wind; Thou meltest me away in the storm.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
I know that thou wilt bring me to death, To the place of assembly for all the living.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
When He stretcheth out his hand, prayer availeth nothing; When He bringeth destruction, vain is the cry for help.
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
Did not I weep for him that was in trouble? Was not my soul grieved for the poor?
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
But when I looked for good, then evil came; When I looked for light, then came darkness.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
My bowels boil, and have no rest; Days of anguish have come upon me.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
I am black, but not by the sun; I stand up, and utter my cries in the congregation.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
I am become a brother to jackals, And a companion to ostriches.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
My skin is black, and falleth from me, And my bones burn with heat.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
My harp also is turned to mourning, And my pipe to notes of grief.

< Ayuba 30 >