< Ayuba 30 >
1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
But now the youngest have laughed me to scorn, now they reprove me in [their] turn, whose fathers I set at nothing; whom I did not deem worthy [to be with] my shepherd dogs.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
Yes, why had I the strength of their hands? for them the full term [of life] was lost.
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
[One is] childless in lack and famine, [such as] they that fled but lately the distress and misery of drought.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
Who compass the salt places on the sounding [shore], who had salt [herbs] for their food, and were dishonorable and of no repute, in lack of every good thing; who also ate roots of trees by reason of great hunger.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
Thieves have risen up against me,
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
whose houses were the caves of the rocks, who lived under the wild shrubs.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
They will cry out among the rustling [bushes].
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
[They are] sons of fools and vile men, [whose] name and glory [are] quenched from off the earth.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
But now I am their music, and they have me for a byword.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
And they stood aloof and abhorred me, and spared not to spit in my face.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
For he has opened his quiver and afflicted me: they also have cast off the restraint of my presence.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
They have risen up against [me] on the right hand of [their] offspring; they have stretched out their foot, and directed against me the ways of their destruction.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
My paths are ruined; for they have stripped off my raiment: he has shot at me with his weapons.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
And he has pleaded against me as he will: I am overwhelmed with pains.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
My pains return upon [me]; my hope is gone like the wind, and my safety as a cloud.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
Even now my life shall be poured forth upon me; and days of anguish seize me.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
And by night my bones are confounded; and my sinews are relaxed.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
With great force [my disease] has taken hold of my garment: it has compassed me as the collar of my coat.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
And you have counted me as clay; my portion in dust and ashes.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
And I have cried to you, but you hear me not: but they stood still, and observed me.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
They attacked me also without mercy: you have scourged me with a strong hand.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
And you have put me to grief, and have cast me away from safety.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
For I know that death will destroy me: for the earth is the house [appointed] for every mortal.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Oh then that I might lay hands upon myself, or at least ask another, and he should do this for me.
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
Yet I wept over every helpless man; I groaned when I saw a man in distress.
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
But I, when I waited for good things, behold, days of evils came the more upon me.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
My belly boiled, and would not cease: the days of poverty prevented me.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
I went mourning without restraint: and I have stood and cried out in the assembly.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
I am become a brother of monsters, and a companion of ostriches.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
And my skin has been greatly blackened, and my bones are burned with heat.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
My harp also has been turned into mourning, and my song into my weeping.