< Ayuba 30 >

1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
But now the younger in time scorn me, whose fathers I would not have set with the dogs of my flock:
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
The strength of whose hands was to me as nothing, and they were thought unworthy of life itself.
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
Barren with want and hunger, who gnawed in the wilderness, disfigured with calamity and misery.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
And they ate grass, and barks of trees, and the root of junipers was their food.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
Who snatched up these things out of the valleys, and when they had found any of them, they ran to them with a cry.
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
They dwelt in the desert places of torrents, and in caves of earth, or upon the gravel.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
They pleased themselves among these kind of things, and counted it delightful to be under the briers.
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
The children of foolish and base men, and not appearing at all upon the earth.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Now I am turned into their song, and am become their byword.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
They abhor me, and flee far from me, and are not afraid to spit in my face.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
For he hath opened his quiver, and hath afflicted me, and hath put a bridle into my mouth.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
At the right hand of my rising, my calamities forthwith arose: they have overthrown my feet, and have overwhelmed me with their paths as with waves.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
They have destroyed my ways, they have lain in wait against me, and they have prevailed, and there was none to help.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
They have rushed in upon me, as when a wall is broken, and a gate opened, and have rolled themselves down to my miseries.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
I am brought to nothing: as a wind thou hast taken away my desire: and my prosperity hath passed away like a cloud.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
And now my soul fadeth within myself, and the days of affliction possess me.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
In the night my bone is pierced with sorrows: and they that feed upon me, do not sleep.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
With the multitude of them my garment is consumed, and they have girded me about, as with the collar of my coat.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
I am compared to dirt, and am likened to embers and ashes.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
I cry to thee, and thou hearest me not: I stand up, and thou dost not regard me.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Thou art changed to be cruel toward me, and in the hardness of thy hand thou art against me.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Thou hast lifted me up, and set me as it were upon the wind, and thou hast mightily dashed me.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
I know that thou wilt deliver me to death, where a house is appointed for every one that liveth.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
But yet thou stretchest not forth thy hand to their consumption: and if they shall fall down thou wilt save.
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
I wept heretofore for him that was afflicted, and my soul had compassion on the poor.
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
I expected good things, and evils are come upon me: I waited for light, and darkness broke out.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
My inner parts have boiled without any rest, the days of affliction have prevented me.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
I went mourning without indignation; I rose up, and cried in the crowd.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
I was the brother of dragons, and companion of ostriches.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
My skin is become black upon me, and my bones are dried up with heat.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
My harp is turned to mourning, and my organ into the voice of those that weep.

< Ayuba 30 >