< Ayuba 30 >

1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
Nyní pak posmívají se mi mladší mne, jejichž bych otců nechtěl byl postaviti se psy stáda svého.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
Ač síla rukou jejich k čemu by mi byla? Zmařena jest při nich starost jejich.
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
Nebo chudobou a hladem znuzeni, utíkali na planá, tmavá, soukromná a pustá místa.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
Kteříž trhali zeliny po chrastinách, ano i koření, a jalovec za pokrm byl jim.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
Z prostřed lidí vyháníni byli; povolávali za nimi, jako za zlodějem,
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
Tak že musili bydliti v výmolích potoků, v děrách země a skálí.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
V chrastinách řvali, pod trní se shromažďovali,
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
Lidé nejnešlechetnější, nýbrž lidé bez poctivosti, menší váhy i než ta země.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Nyní, pravím, jsem jejich písničkou, jsa jim učiněn za přísloví.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
V ošklivosti mne mají, vzdalují se mne, a na tvář mou nestydí se plvati.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Nebo Bůh mou vážnost odjal, a ssoužil mne; pročež uzdu před přítomností mou svrhli.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
Po pravici mládež povstává, nohy mi podrážejí, tak že šlapáním protřeli ke mně stezky nešlechetnosti své.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Mou pak stezku zkazili, k bídě mé přidali, ač jim to nic nepomůže.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Jako širokou mezerou vskakují, a k vyplénění mému valí se.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Obrátily se na mne hrůzy, stihají jako vítr ochotnost mou, nebo jako oblak pomíjí zdraví mé.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
A již ve mně rozlila se duše má, pochytili mne dnové trápení mého,
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
Kteréž v noci vrtá kosti mé ve mně; pročež ani nervové moji neodpočívají.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Oděv můj mění se pro násilnou moc bolesti, kteráž mne tak jako obojek sukně mé svírá.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Uvrhl mne do bláta, tak že jsem již podobný prachu a popelu.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Volám k tobě, ó Bože, a neslyšíš mne; postavuji se, ale nehledíš na mne.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Obrátils mi se v ukrutného nepřítele, silou ruky své mi odporuješ.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Vznášíš mne u vítr, sázíš mne na něj, a k rozplynutí mi přivodíš zdravý soud.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Nebo vím, že mne k smrti odkážeš, a do domu, do něhož se shromažďuje všeliký živý.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Jistě žeť nevztáhne Bůh do hrobu ruky, by pak, když je stírá, i volali.
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
Zdaliž jsem neplakal nad tím, kdož okoušel zlých dnů? Duše má kormoutila se nad nuzným.
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
Když jsem dobrého čekal, přišlo mi zlé; nadál jsem se světla, ale přišla mrákota.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
Vnitřností mé zevřely, tak že se ještě neupokojily; předstihli mne dnové trápení.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Chodím osmahlý, ne od slunce, povstávaje, i mezi mnohými křičím.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
Bratrem učiněn jsem draků, a tovaryšem mladých pstrosů.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Kůže má zčernala na mně, a kosti mé vyprahly od horkosti.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
A protož v kvílení obrátila se harfa má, a píšťalka má v hlas plačících.

< Ayuba 30 >