< Ayuba 3 >

1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
Oluvannyuma lw’ebyo, Yobu n’ayasamya akamwa ke n’akolimira olunaku kwe yazaalirwa.
2 Ayuba ya ce,
N’agamba nti,
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
“Olunaku kwe nazaalirwa luzikirire, n’ekiro lwe kyalangirirwa nti omwana mulenzi.
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Olunaku olwo lubuutikirwe ekizikiza, omusana guleme okulwakako, Katonda aleme okulufaako.
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Ekizikiza n’ekisiikirize eky’okufa birujjule, ekire kirutuuleko, ekizikiza kikankanye ekitangaala kyalwo.
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
Ekizikiza ekikutte be zigizigi kirunyage, luleme okubalirwa awamu n’ennaku eziri mu mwaka, wadde okuyingizibwa mu ezo eziri mu mwezi.
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Yee, lubeere lugumba, waleme okuba eddoboozi lyonna ery’essanyu eririwulirwako.
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
Abo abakolimira ennyanja n’ennaku balukolimire, n’abo abamanyi okuzuukusa agasolo galukwata mu nnyanja, balukolimire.
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Emmunyeenye ez’omu matulutulu gaalwo zibe ekizikiza, lulindirire ekitangaala kirubulwe, luleme okulaba ebikowe by’oku nkya.
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
Kubanga terwaggala nzigi za lubuto lwa mmange, nneme okulaba obuyinike.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
“Lwaki saafa nga nzalibwa, oba ne nfa nga nva mu lubuto lwa mmange?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Lwaki amaviivi ganzikiriza okugatuulako era n’amabeere okugayonka?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
Kaakano nandibadde ngalamidde nga neesirikidde, nandibadde neebase nga neewummulidde,
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
wamu ne bakabaka n’abakungu ab’ensi, abezimbira embiri kaakano amatongo,
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
oba n’abalangira abaalina zaabu, abajjuzanga ffeeza mu nnyumba zaabwe.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Oba lwaki saaziikibwa ng’omwana azaaliddwa ng’afudde, atalabye ku kitangaala?
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
Eyo ababi gye batatawaanyizibwa, era n’abakooye gye bawummulira.
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
Abasibe gye bawummulira awamu, gye batawulirira kiragiro ky’oyo abaduumira.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
Abakopi n’abakungu gye babeera; abaddu gye batatuntuzibwa bakama baabwe.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
“Lwaki omuyinike aweebwa ekitangaala, ne kimulisiza oyo alumwa mu mwoyo,
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
era lwaki yeegomba okufa naye ne kutajja, n’akunoonya okusinga obugagga obuziikiddwa,
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
abajaguza ekisukkiridde, ne basanyuka ng’atuuse ku ntaana?
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
Lwaki okuwa ekitangaala oyo, atayinza kulaba kkubo, Katonda gw’akomedde?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
Kubanga nkaaba mu kifo ky’okulya, n’okusinda kwange kufukumuka ng’amazzi.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
Ekintu kye nantiiranga ddala era kye nakyawa kye kyantukako.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
Siwummudde wadde okusiriikirira wadde okuba n’emirembe, wabula buzibu bwereere bwe bunzijidde.”

< Ayuba 3 >