< Ayuba 3 >

1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
Dopo, Giobbe aprì la bocca e maledisse il suo giorno;
2 Ayuba ya ce,
prese a dire:
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
Perisca il giorno in cui nacqui e la notte in cui si disse: «E' stato concepito un uomo!».
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Quel giorno sia tenebra, non lo ricerchi Dio dall'alto, né brilli mai su di esso la luce.
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Lo rivendichi tenebra e morte, gli si stenda sopra una nube e lo facciano spaventoso gli uragani del giorno!
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
Quel giorno lo possieda il buio non si aggiunga ai giorni dell'anno, non entri nel conto dei mesi.
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Ecco, quella notte sia lugubre e non entri giubilo in essa.
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
La maledicano quelli che imprecano al giorno, che sono pronti a evocare Leviatan.
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Si oscurino le stelle del suo crepuscolo, speri la luce e non venga; non veda schiudersi le palpebre dell'aurora,
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
poiché non mi ha chiuso il varco del grembo materno, e non ha nascosto l'affanno agli occhi miei!
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
E perché non sono morto fin dal seno di mia madre e non spirai appena uscito dal grembo?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Perché due ginocchia mi hanno accolto, e perché due mammelle, per allattarmi?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
Sì, ora giacerei tranquillo, dormirei e avrei pace
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
con i re e i governanti della terra, che si sono costruiti mausolei,
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
o con i principi, che hanno oro e riempiono le case d'argento.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Oppure, come aborto nascosto, più non sarei, o come i bimbi che non hanno visto la luce.
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
Laggiù i malvagi cessano d'agitarsi, laggiù riposano gli sfiniti di forze.
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
I prigionieri hanno pace insieme, non sentono più la voce dell'aguzzino.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
Laggiù è il piccolo e il grande, e lo schiavo è libero dal suo padrone.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Perché dare la luce a un infelice e la vita a chi ha l'amarezza nel cuore,
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
a quelli che aspettano la morte e non viene, che la cercano più di un tesoro,
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
che godono alla vista di un tumulo, gioiscono se possono trovare una tomba...
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
a un uomo, la cui via è nascosta e che Dio da ogni parte ha sbarrato?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
Così, al posto del cibo entra il mio gemito, e i miei ruggiti sgorgano come acqua,
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
perché ciò che temo mi accade e quel che mi spaventa mi raggiunge.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
Non ho tranquillità, non ho requie, non ho riposo e viene il tormento!

< Ayuba 3 >