< Ayuba 3 >

1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
Après cela Job ouvrit la bouche, et maudit le jour de sa naissance.
2 Ayuba ya ce,
Et il parla.
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
Périsse le jour auquel je suis né, et la nuit dans laquelle il fut dit: Un homme a été conçu!
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Que ce jour soit changé en ténèbres; que Dieu ne s’en enquière pas d’en haut, et qu’il ne soit point éclairé de la lumière.
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Que des ténèbres et une ombre de mort l’obscurcissent; qu’une obscurité s’en empare, et qu’il soit enveloppé d’amertume.
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
Cette nuit, qu’un tourbillon ténébreux en prenne possession, qu’elle ne soit pas comptée dans les jours de l’année, ni mise au nombre des mois.
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Que cette nuit soit solitaire, et qu’elle ne mérite pas de louanges.
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
Qu’ils la maudissent, ceux qui maudissent le jour, qui sont prêts à susciter Léviathan.
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Que les étoiles soient couvertes des ténèbres de son obscurité; qu’elle attende une lumière, et ne la voie point, ni la naissance de l’aurore qui se lève;
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
Parce qu’elle n’a pas fermé le sein qui ma formé, et qu’elle n’a pas ôté les maux de devant mes yeux.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Pourquoi ne suis-je pas mort dans le sein de ma mère? pourquoi, sorti de son sein, n’ai-je pas aussitôt péri?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Pourquoi ai-je été reçu sur des genoux? pourquoi allaité par des mamelles?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
Car maintenant, dormant, je serais en silence, et je reposerais dans mon sommeil,
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
Avec les rois et les consuls; de la terre, qui se bâtissent de vastes solitudes;
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
Avec les princes qui possèdent de l’or, et remplissent leurs maisons d’argent.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Ou bien je n’existerais pas, comme un avorton caché dans le sein de sa mère, ou comme ceux qui, conçus, n’ont pas vu la lumière.
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
C’est là que des impies ont cessé leur tumulte, et là que se reposent ceux qui ont perdu leur force.
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
Et ceux qui autrefois étaient enchaînes ensemble sont sans inquiétude; ils n’entendent pas la voix d’un exacteur.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
Des grands et des petits sont là, et un esclave est délivré de son maître.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Pourquoi la lumière a-t-elle été donnée aux malheureux, et la vie à ceux qui sont dans l’amertume de l’âme,
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
Qui attendent la mort (et elle ne vient pas), comme s’ils déterraient un trésor,
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
Et qui se réjouissent extrêmement, lorsqu’ils ont trouvé un sépulcre;
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
À un homme dont la voie est cachée, et que Dieu entoure de ténèbres?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
Avant que je mange, je soupire; et comme les eaux qui débordent, ainsi sont mes rugissements,
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
Parce que la frayeur que je redoutais m’est venue, et ce que j’appréhendais est arrivé.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
N’ai-je pas dissimulé? n’ai-je pas gardé le silence? ne suis-je pas resté dans le repos? Cependant l’indignation de Dieu est venue sur moi.

< Ayuba 3 >