< Ayuba 3 >

1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
Après cela, Job ouvrit la bouche, et maudit son jour.
2 Ayuba ya ce,
Car prenant la parole, il dit:
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
Périsse le jour auquel je naquis, et la nuit en laquelle il fut dit: Un enfant mâle est né!
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Que ce jour-là ne soit que ténèbres; que Dieu ne le recherche point d'en haut, et qu'il ne soit point éclairé de la lumière!
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Que les ténèbres et l'ombre de la mort le rendent souillé; que les nuées demeurent sur lui; qu'il soit rendu terrible comme le jour de ceux à qui la vie est amère!
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
Que l'obscurité couvre cette nuit-là, qu'elle ne se réjouisse point d'être parmi les jours de l'année, et qu'elle ne soit point comptée parmi les mois!
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Voilà, que cette nuit soit solitaire, qu'on ne se réjouisse point en elle!
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
Que ceux qui [ont accoutumé] de maudire les jours et ceux qui sont prêts à renouveler leur deuil, la maudissent!
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Que les étoiles de son crépuscule soient obscurcies; qu'elle attende la lumière, mais qu'il n'y en ait point, et qu'elle ne voie point les rayons de l'aube du jour!
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
Parce qu'elle n'a pas fermé le ventre qui m'a porté, et qu'elle n'a point caché le tourment loin de mes yeux.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Que ne suis-je mort dès la matrice; que n'ai-je expiré aussitôt que je suis sorti du ventre [de ma mère]!
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Pourquoi les genoux m'ont-ils reçu? pourquoi [m'a-t-on présenté] les mamelles afin que je les suçasse?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
Car maintenant je serais couché, je me reposerais, je dormirais; il y aurait eu dès lors du repos pour moi,
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
Avec les Rois et les Gouverneurs de la terre, qui se bâtissent des solitudes;
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
Ou avec les Princes qui ont eu de l'or, [et] qui ont rempli d'argent leurs maisons.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Ou que n'ai-je été comme un avorton caché; comme les petits enfants qui n'ont point vu la lumière!
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
Là les méchants ne tourmentent plus [personne], et là demeurent en repos ceux qui ont perdu leur force.
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
Pareillement ceux qui avaient été dans les liens, jouissent [là] du repos, et n'entendent plus la voix de l'exacteur.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
Le petit et le grand sont là; [et là] l'esclave n'est plus sujet à son seigneur.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Pourquoi la lumière est-elle donnée au misérable, et la vie à ceux qui ont le cœur dans l'amertume;
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
Qui attendent la mort, et elle ne vient point, et qui la recherchent plus que les trésors;
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
Qui seraient ravis de joie [et] seraient dans l'allégresse, s'ils avaient trouvé le sépulcre?
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
[Pourquoi, dis-je, la lumière est-elle donnée] à l'homme à qui le chemin est caché, et que Dieu a enfermé de tous côtés?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
Car avant que je mange, mon soupir vient, et mes rugissements coulent comme des eaux.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
Parce que ce que je craignais le plus, m'est arrivé, et ce que j'appréhendais, m'est survenu.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
Je n'ai point eu de paix, je n'ai point eu de repos, ni de calme, depuis que ce trouble m'est arrivé.

< Ayuba 3 >