< Ayuba 3 >
1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
Après cela, Job ouvrit la bouche et maudit le jour de sa naissance.
Il prit la parole et dit:
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
Périsse le jour où je suis né, Et la nuit qui dit: Un enfant mâle est conçu!
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Ce jour! Qu’il se change en ténèbres, Que Dieu n’en ait point souci dans le ciel, Et que la lumière ne rayonne plus sur lui!
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Que l’obscurité et l’ombre de la mort s’en emparent, Que des nuées établissent leur demeure au-dessus de lui, Et que de noirs phénomènes l’épouvantent!
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
Cette nuit! Que les ténèbres en fassent leur proie, Qu’elle disparaisse de l’année, Qu’elle ne soit plus comptée parmi les mois!
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Que cette nuit devienne stérile, Que l’allégresse en soit bannie!
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
Qu’elle soit maudite par ceux qui maudissent les jours, Par ceux qui savent exciter le léviathan!
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Que les étoiles de son crépuscule s’obscurcissent, Qu’elle attende en vain la lumière, Et qu’elle ne voie point les paupières de l’aurore!
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
Car elle n’a pas fermé le sein qui me conçut, Ni dérobé la souffrance à mes regards.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Pourquoi ne suis-je pas mort dans le ventre de ma mère? Pourquoi n’ai-je pas expiré au sortir de ses entrailles?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Pourquoi ai-je trouvé des genoux pour me recevoir, Et des mamelles pour m’allaiter?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
Je serais couché maintenant, je serais tranquille, Je dormirais, je reposerais,
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
Avec les rois et les grands de la terre, Qui se bâtirent des mausolées,
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
Avec les princes qui avaient de l’or, Et qui remplirent d’argent leurs demeures.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Ou je n’existerais pas, je serais comme un avorton caché, Comme des enfants qui n’ont pas vu la lumière.
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
Là ne s’agitent plus les méchants, Et là se reposent ceux qui sont fatigués et sans force;
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
Les captifs sont tous en paix, Ils n’entendent pas la voix de l’oppresseur;
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
Le petit et le grand sont là, Et l’esclave n’est plus soumis à son maître.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Pourquoi donne-t-il la lumière à celui qui souffre, Et la vie à ceux qui ont l’amertume dans l’âme,
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
Qui espèrent en vain la mort, Et qui la convoitent plus qu’un trésor,
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
Qui seraient transportés de joie Et saisis d’allégresse, s’ils trouvaient le tombeau?
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
A l’homme qui ne sait où aller, Et que Dieu cerne de toutes parts?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
Mes soupirs sont ma nourriture, Et mes cris se répandent comme l’eau.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
Ce que je crains, c’est ce qui m’arrive; Ce que je redoute, c’est ce qui m’atteint.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
Je n’ai ni tranquillité, ni paix, ni repos, Et le trouble s’est emparé de moi.